< Salme 50 >

1 (En salme af Asaf.) Gud, Gud HERREN talede og stævnede Jorden hid fra Sol i Opgang til Sol i Bjærge;
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 fra Zion, Skønhedens Krone, viste Gud sig i Stråleglans
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 vor Gud komme og tie ikke! - Foran ham gik fortærende Ild, omkring ham rasede Storm;
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 han stævnede Himlen deroppe hid og Jorden for at dømme sit Folk:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 "Saml mig mine fromme, der sluttede Pagt med mig ved Ofre!"
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Og Himlen forkyndte hans Retfærd, at Gud er den, der dømmer. (Sela)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Hør, mit Folk, jeg vil tale, Israel, jeg vil vidne imod dig, Gud, din Gud er jeg!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Jeg laster dig ikke for dine Slagtofre, dine Brændofre har jeg jo stadig for Øje;
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 jeg tager ej Tyre fra dit Hus eller Bukke fra dine Stalde;
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 thi mig tilhører alt Skovens Vildt, Dyrene på de tusinde Bjerge;
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 jeg kender alle Bjergenes Fugle, har rede på Markens Vrimmel.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Om jeg hungred, jeg sagde det ikke til dig, thi mit er Jorderig og dets Fylde!
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Mon jeg æder Tyres Kød eller drikker Bukkes Blod?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Lovsang skal du ofre til Gud og holde den Højeste dine Løfter.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Og kald på mig på Nødens Dag; jeg vil udfri dig, og du skal ære mig,
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Men til Den gudløse siger Gud: Hvi regner du op mine Bud og fører min Pagt i Munden,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 når du dog hader Tugt og kaster mine Ord bag din Ryg?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Ser du en Tyv, slår du Følge med ham, med Horkarle bolder du til,
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 slipper Munden løs med ondt, din Tunge bærer på Svig.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Du sidder og skænder din Broder, bagtaler din Moders Søn;
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 det gør du, og jeg skulde tie, og du skulde tænke, jeg er som du! Revse dig vil jeg og gøre dig det klart.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Mærk jer det, I, som glemmer Gud, at jeg ikke skal rive jer redningsløst sønder.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Den, der ofrer Taksigelse, ærer mig; den, der agter på Vejen, lader jeg se Guds Frelse.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Salme 50 >