< Salme 37 >

1 (Af David.) Græm dig ikke over Ugerningsmænd, misund ikke dem, der gør Uret!
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 Thi hastigt svides de af som Græsset, visner som det friske Grønne.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Stol på HERREN og gør det gode, bo i Landet og læg Vind på Troskab,
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 da skal du have din Fryd i HERREN, og han skal give dig, hvad dit Hjerte attrår.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Vælt din Vej på HERREN, stol på ham, så griber han ind
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 og fører din Retfærdighed frem som Lyset, din Ret som den klare Dag.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Vær stille for HERREN og bi på ham, græm dig ej over den, der har Held, over den, der farer med Rænker.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Tæm din Harme, lad Vreden fare, græm dig ikke, det volder kun Harm.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 Thi Ugerningsmænd skal ryddes ud, men de, der bier på HERREN, skal arve Landet.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 En liden Stund, og den gudløse er ikke mere; ser du hen til hans Sted, så er han der ikke.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 Men de sagtmodige skal arve Landet, de fryder sig ved megen Fred.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 Den gudløse vil den retfærdige ilde og skærer Tænder imod ham;
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 men Herren, han ler ad ham, thi han ser hans Time komme.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 De gudløse drager Sværdet og spænder Buen for at fælde arm og fattig, for at nedslagte dem, der vandrer ret;
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 men Sværdet rammer dem selv i Hjertet, og Buerne brydes sønder og sammen.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Det lidt, en retfærdig har, er bedre end mange gudløses Rigdom;
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 thi de gudløses Arme skal brydes, men HERREN støtter de retfærdige;
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 HERREN kender de uskyldiges Dage, deres Arvelod bliver evindelig;
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 de beskæmmes ikke i onde Tider, de mættes i Hungerens Dage.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 Thi de gudløse går til Grunde, som Engenes Pragt er HERRENs Fjender, de svinder, de svinder som Røg.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 Den gudløse låner og bliver i Gælden, den retfærdige ynkes og giver;
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 de, han velsigner, skal arve Landet, de, han forbander, udryddes.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 Af HERREN stadfæstes Mandens Skridt, når han har Behag i hans Vej;
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 om end han snubler, falder han ikke, thi HERREN støtter hans Hånd.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Ung har jeg været, og nu er jeg gammel, men aldrig så jeg en retfærdig forladt eller hans Afkom tigge sit Brød;
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 han ynkes altid og låner ud, og hans Afkom er til Velsignelse.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Vig fra ondt og øv godt, så bliver du boende evindelig;
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 thi HERREN elsker Ret og svigter ej sine fromme. De onde udslettes for evigt, de gudløses Afkom udryddes;
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 de retfærdige arver Landet og skal bo der til evig Tid.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 Den retfærdiges Mund taler Visdom; hans Tunge siger, hvad ret er;
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 sin Guds Lov har han i Hjertet, ikke vakler hans Skridt.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 Den gudløse lurer på den retfærdige og står ham efter Livet,
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 men, HERREN giver ham ej i hans Hånd og lader ham ikke dømmes for Retten.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Bi på HERREN og bliv på hans Vej, så skal han ophøje dig til at arve Landet; du skal skue de gudløses Undergang.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 Jeg har set en gudløs trodse, bryste sig som en Libanons Ceder
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 men se, da jeg gik der forbi, var han borte; da jeg søgte ham, fandtes han ikke.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Vogt på Uskyld, læg Vind på Oprigtighed, thi Fredens Mand har en Fremtid;
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 men Overtræderne udryddes til Hobe, de gudløses Fremtid går tabt.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 De retfærdiges Frelse kommer fra HERREN, deres Tilflugt i Nødens Stund;
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 HERREN hjælper og frier dem, fra de gudløse frier og frelser han dem; thi hos ham har de søgt deres Tilflugt.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Salme 37 >