< Salme 3 >
1 (En Salme af David, da han flygtede for sin søn Absalom.) HERRE, hvor er mine Fjender mange! Mange er de, som rejser sig mod mig,
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 mange, som siger om min Sjæl: "Der er ingen Frelse for ham hos Gud!" (Sela)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 Men, HERRE, du er et Skjold for mig, min Ære og den, der løfter mit Hoved.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 Jeg råber højlydt til HERREN, han svarer mig fra sit hellige Bjerg. (Sela)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 Jeg lagde mig og sov ind, jeg vågned, thi HERREN holder mig oppe.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 Jeg frygter ikke Titusinder af Folk, som trindt om lejrer sig mod mig.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Rejs dig, HERRE, frels mig, min Gud, thi alle mine Fjender slog du på Kind, du brød de gudløses Tænder!
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Hos HERREN er Frelsen; din Velsignelse over dit Folk! (Sela)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)