< Salme 25 >

1 (Af David.) HERRE, jeg løfter min sjæl til dig
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 min Gud jeg stoler på dig, lad mig ikke beskæmmes, lad ej mine Fjender fryde sig over mig.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Nej, ingen som bier på dig, skal beskæmmes; beskæmmes skal de, som er troløse uden Grund.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Lad mig kende dine Veje, HERRE lær mig dine Stier.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Led mig på din Sandheds Vej og lær mig, thi du er min Frelses Gud; jeg bier bestandig på dig.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 HERRE, kom din Barmhjertighed i Hu og din Nåde, den er jo fra Evighed af.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Mine Ungdomssynder og Overtrædelser komme du ikke i Hu, men efter din Miskundhed kom mig i Hu, for din Godheds Skyld, o HERRE!
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 God og oprigtig er HERREN, derfor viser han Syndere Vejen.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Han vejleder ydmyge i det, som er ret, og lærer de ydmyge sin Vej.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Alle HERRENs Stier er Miskundhed og Trofasthed for dem, der holder hans Pagt og hans Vidnesbyrd.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For dit Navns Skyld, HERRE, tilgive du min Brøde, thi den er stor.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Om nogen frygter HERREN, ham viser han den Vej, han skal vælge;
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 selv skal han leve i Lykke og hans Sæd få Landet i Eje.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 Fortroligt Samfund har HERREN med dem, der frygter ham, og han kundgør dem sin Pagt.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mit Øje er stadig vendt imod HERREN, thi han frier mine Fødder af Snaren.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Vend dig til mig og vær mig nådig, thi jeg er ene og arm.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Let mit Hjertes Trængsler og før mig ud af min Nød.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Se hen til min Nød og min Kvide og tilgiv alle mine Synder.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Se hen til mine Fjender, thi de er mange og hader mig med Had uden Grund.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Vogt min Sjæl og frels mig, jeg lider på dig, lad mig ikke beskæmmes.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Lad Uskyld og Retsind vogte mig, thi jeg bier på dig, HERRE.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Forløs, o Gud, Israel af alle dets Trængsler!
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Salme 25 >