< Salme 18 >
1 (Til sangmesteren. Af HERRENS tjener David, som sang HERREN denne sang, dengang HERREN havde frelst ham af alle hans fjenders og af Sauls hånd. Han sang: ) HERRE, jeg har dig hjerteligt kær, min Styrke!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 HERRE, min Klippe, min Borg. min Befrier, min Gud, mit Bjerg, hvortil jeg tyr, mit Skjold, mit Frelseshorn, mit Værn!
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 Jeg påkalder HERREN, den Højlovede, og frelses fra mine Fjender.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Dødens Reb omsluttede mig, Ødelæggelsens Strømme forfærdede mig,
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Dødsrigets Reb omspændte mig, Dødens Snarer faldt over mig; (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 i min Vånde påkaldte jeg HERREN og råbte til min Gud. Han hørte min Røst fra sin Helligdom, mit Råb fandt ind til hans Ører!
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Da rystede Jorden og skjalv, Bjergenes Grundvolde bæved og rysted, thi hans Vrede blussede op.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 Røg for ud af hans Næse, fortærende Ild af hans Mund, Gløder gnistrede fra ham.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Han sænkede Himlen, steg ned med Skymulm under sine Fødder;
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 båret af Keruber fløj han, svæved på Vindens Vinger;
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 han omgav sig med Mulm som en Bolig, mørke Vandmasser, vandfyldte Skyer.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 Fra Glansen foran ham for der Hagl og Ildgløder gennem hans Skyer.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 HERREN tordnede fra Himlen, den Højeste lod høre sin Røst, Hagl og Ildgløder.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 Han udslyngede Pile, adsplittede dem, Lyn i Mængde og skræmmede dem.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Vandenes Bund kom til Syne, Jordens Grundvolde blottedes ved din Trusel, HERRE, for din Vredes Pust.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 Han udrakte Hånden fra det høje og greb mig, drog mig op af de vældige Vande,
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 frelste mig fra mine mægtige Fjender, fra mine Avindsmænd; de var mig for stærke.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 På min Ulykkes Dag faldt de over mig, men HERREN blev mig til Værn.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 Han førte mig ud i åbent Land, han frelste mig, thi han havde Behag i mig.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 HERREN gengældte mig efter min Retfærd, lønned mig efter mine Hænders Uskyld;
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 thi jeg holdt mig til HERRENs Veje, svigted i Gudløshed ikke min Gud
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 hans Bud stod mig alle for Øje, hans Lov skød jeg ikke fra mig.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 Ustraffelig var jeg for ham og vogtede mig for Brøde.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 HERREN lønned mig efter min Retfærd, mine Hænders Uskyld, som stod ham for Øje!
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Du viser dig from mod den fromme, retsindig mod den retsindige,
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 du viser dig ren mod den rene og vrang mod den svigefulde.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 De arme giver du Frelse, hovmodiges Øjne Skam!
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 Ja, min Lampe lader du lyse, HERRE, min Gud opklarer mit Mørke.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 Thi ved din Hjælp søndrer jeg Mure, ved min Guds Hjælp springer jeg over Volde.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Fuldkommen er Guds Vej, lutret er HERRENs Ord. Han er et Skjold for alle, der sætter deres Lid til ham.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Ja, hvem er Gud uden HERREN, hvem er en Klippe uden vor Gud,
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 den Gud, der omgjorded mig med Kraft, jævnede Vejen for mig,
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 gjorde mine Fødder som Hindens og gav mig Fodfæste på Højene,
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 oplærte min Hånd til Krig, så mine Arme spændte Kobberbuen!
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Du gav mig din Frelses Skjold, din højre støttede mig, din Nedladelse gjorde mig stor;
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 du skaffede Plads for mine Skridt, mine Ankler vaklede ikke.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 Jeg jog mine Fjender, indhentede dem, vendte først om, da de var gjort til intet,
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 slog dem ned, så de ej kunde rejse sig, men lå faldne under min Fod.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Du omgjorded mig med Kraft til Kampen, mine Modstandere tvang du i Knæ for mig;
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 du slog mine Fjender på Flugt, mine Avindsmænd rydded jeg af Vejen.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 De råbte, men ingen hjalp, til HERREN, han svared dem ikke.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Jeg knuste dem som Støv for Vinden, fejed dem bort som Gadeskarn.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Du friede mig af Folkekampe, du satte mig til Folkeslags Høvding; nu tjener mig ukendte Folk;
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 hører de om mig, lyder de mig, Udlandets Sønner kryber for mig;
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Udlandets Sønner vansmægter, slæber sig frem af deres Skjul.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 HERREN lever, højlovet min Klippe, ophøjet være min Frelses Gud,
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 den Gud, som giver mig Hævn, tvinger Folkeslag under min Fod
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 og frier mig fra mine vrede Fjender! Du ophøjer mig over mine Modstandere, fra Voldsmænd frelser du mig.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 HERRE, derfor priser jeg dig blandt Folkene og lovsynger dit Navn,
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 du, som kraftig hjælper din Konge og viser din Salvede Miskundhed, David og hans Æt evindelig.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.