< Salme 17 >
1 (En bøn af David.) HERRE, hør en retfærdig Sag, lyt til min Klage lån Øre til Bøn fra svigløse Læber!
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Fra dig skal min Ret udgå, thi hvad ret er, ser dine Øjne.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Prøv mit Hjerte, se efter om Natten, ransag mig, du finder ej Svig hos mig.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Ej synded min Mund, hvad end Mennesker gjorde; ved dine Læbers Ord vogted jeg mig for Voldsmænds Veje;
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 mine Skridt har holdt dine Spor, jeg vaklede ej på min Gang.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 Jeg råber til dig, thi du svarer mig, Gud, bøj Øret til mig, hør på mit Ord!
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Vis, dig underfuldt nådig, du Frelser for dem, der tyr til din højre for Fjender!
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Vogt mig som Øjestenen, skjul mig i dine Vingers Skygge
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 for gudløse, der øver Vold imod mig, glubske Fjender, som omringer mig;
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 de har lukket deres Hjerte med Fedt, deres Mund fører Hovmodstale.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 De omringer os, overalt hvor vi går, de sigter på at slå os til Jorden.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 De er som den rovgridske Løve, den unge Løve, der ligger på Lur.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Rejs dig, HERRE, træd ham i Møde, kast ham til Jorden, fri med dit Sværd min Sjæl fra den gudløses Vold,
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 fra Mændene, HERRE, med din Hånd, fra dødelige Mænd - lad dem få deres Del i levende Live! Fyld deres Bug med dit Forråd af Vrede, lad Børnene mættes dermed og efterlade deres Børn, hvad de levner!
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Men jeg skal i Retfærd skue dit Åsyn, mættes ved din Skikkelse, når jeg vågner.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.