< Salme 109 >

1 (Til Sangmesteren. Af David. En Salme.) Du min Lovsangs Gud, vær ej tavs!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Thi en gudløs, svigefuld Mund har de åbnet imod mig, taler mig til med Løgntunge,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 med hadske Ord omringer de mig og strider imod mig uden Grund;
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 til Løn for min Kærlighed er de mig fjendske, skønt jeg er idel Bøn;
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 de gør mig ondt for godt, gengælder min Kærlighed med Had.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Straf ham for hans Gudløshed, lad en Anklager stå ved hans højre,
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 lad ham gå dømt fra Retten, hans Bøn blive regnet for Synd;
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 hans Livsdage blive kun få, hans Embede tage en anden;
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 hans Børn blive faderløse, hans Hustru vorde Enke;
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 hans Børn flakke om og tigge, drives bort fra et øde Hjem;
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Ågerkarlen rage efter alt, hvad han har, og fremmede rane hans Gods;
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 ingen være langmodig imod ham, ingen ynke hans faderløse;
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 hans Afkom gå til Grunde, hans Navn slettes ud i næste Slægt:
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 lad hans Fædres Skyld ihukommes hos HERREN, lad ikke hans Moders Synd slettes ud,
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 altid være de, HERREN for Øje; hans Minde vorde udryddet af Jorden,
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 fordi det ej faldt ham ind at vise sig god, men han forfulgte den arme og fattige og den, hvis Hjerte var knust til Døde;
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 han elsked Forbandelse, så lad den nå ham; Velsignelse yndede han ikke, den blive ham fjern!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Han tage Forbandelse på som en Klædning, den komme som Vand i hans Bug, som Olie ind i hans Ben;
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 den blive en Dragt, han tager på, et Bælte, han altid bærer!
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Det være mine Modstanderes Løn fra HERREN, dem, der taler ondt mod min Sjæl.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Men du, o HERRE, min Herre, gør med mig efter din Godhed og Nåde, frels mig for dit Navns Skyld!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Thi jeg er arm og fattig, mit Hjerte vånder sig i mig;
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 som Skyggen, der hælder, svinder jeg bort, som Græshopper rystes jeg ud;
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 af Faste vakler mine Knæ, mit Kød skrumper ind uden Salve;
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 til Spot for dem er jeg blevet, de ryster på Hovedet, når de
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Hjælp mig, HERRE min Gud, frels mig efter din Miskundhed,
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 så de sander, det var din Hånd, dig, HERRE, som gjorde det!
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Lad dem forbande, du vil velsigne, mine uvenner vorde til Skamme, din Tjener glæde sig;
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 lad mine Fjender klædes i Skændsel, iføres Skam som en Kappe!
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Med min Mund vil jeg højlig takke HERREN, prise ham midt i Mængden;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 thi han står ved den fattiges højre at fri ham fra dem, der dømmer hans Sjæl.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Salme 109 >