< Salme 107 >
1 Halleluja! Lov Herren, thi han er god, thi hans Miskundhed varer evindelig!
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Så skal HERRENs genløste sige, de, han løste af Fjendens Hånd
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 og samlede ind fra Landene, fra Øst og Vest, fra Nord og fra Havet.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 I den øde Ørk for de vild, fandt ikke Vej til beboet By,
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 de led både Sult og Tørst, deres Sjæl var ved at vansmægte;
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 men de råbte til HERREN i Nøden, han frelste dem at deres Trængsler
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 og førte dem ad rette Vej, så de kom til beboet By.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Lad dem takke HERREN for hans Miskundhed, for hans Underværker mod Menneskens Børn.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Thi han mættede den vansmægtende Sjæl og fyldte den sultne med godt.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 De sad i Mulm og Mørke, bundne i pine og Jern,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 fordi de havde stået Guds Ord imod og ringeagtet den Højestes Råd.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Deres Hjerte var knuget af Kummer, de faldt, der var ingen, som hjalp;
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 men de råbte til HERREN i Nøden, han frelste dem af deres Trængsler,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 førte dem ud af Mørket og Mulmet og sønderrev deres Bånd.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Lad dem takke HERREN for hans Miskundhed, for hans Underværker mod Menneskens Børn.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Thi han sprængte Døre af Kobber og sønderslog Slåer af Jern.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 De sygnede hen for Synd og led for Brødes Skyld,
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 de væmmedes ved al Slags Mad, de kom Dødens Porte nær
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 men de råbte til Herren i Nøden, han frelste dem af deres Trængsler,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 sendte sit Ord og lægede dem og frelste deres Liv fra Graven.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Lad dem takke HERREN for hans Miskundhed, for hans Underværker mod Menneskens Børn
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 og ofre Lovprisningsofre og med Jubel forkynnde hans Gerninger.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 De for ud på Havet i Skibe, drev Handel på vældige Vande,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 blev Vidne til HERRENs Gerninger, hans Underværker i Dybet;
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 han bød, og et Stormvejr rejste sig, Bølgerne tårnedes op;
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 mod Himlen steg de, i Dybet sank de, i Ulykken svandt deres Mod;
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 de tumled og raved som drukne, borte var al deres Visdom;
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 men de råbte til HERREN i Nøden, han frelste dem af deres Trængsler,
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 skiftede Stormen til Stille, så Havets Bølger tav;
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 og glade blev de, fordi det stilned; han førte dem til Havnen, de søgte.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Lad dem takke HERREN for hans Miskundhed, for hans Underværker mod Menneskens Børn,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 ophøje ham i Folkets Forsamling og prise ham i de Ældstes Kreds!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Floder gør han til Ørken og Kilder til øde Land,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 til Saltsteppe frugtbart Land for Ondskabens Skyld hos dem, som - bor der.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Ørken gør han til Vanddrag, det tørre Land til Kilder;
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 der lader han sultne bo, så de grunder en By at bo i,
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 tilsår Marker og planter Vin og høster Afgrødens Frugt.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Han velsigner dem, de bliver mange, han lader det ikke skorte på Kvæg.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 De bliver få og segner under Modgangs og Kummers Tryk,
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 han udøser Hån over Fyrster og lader dem rave i vejløst Øde.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Men han løfter den fattige op af hans Nød og gør deres Slægter som Hjorde;
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 de oprigtige ser det og glædes, men al Ondskab lukker sin Mund.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Hvo som er viis, han mærke sig det og lægge sig HERRENs Nåde på Sinde!
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.