< Salme 105 >

1 Pris Herren, påkald hans navn, gør hans Gerninger kendte blandt Folkeslag!
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Syng og spil til hans Pris, tal om alle hans Undere;
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 ros jer af hans hellige Navn, eders Hjerte glæde sig, I, som søger HERREN;
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 spørg efter HERREN og hans magt, søg bestandig hans Åsyn;
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 kom i Hu de Undere, han gjorde, hans Tegn og hans Munds Domme,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 I, hans Tjener Abrahams Sæd, hans udvalgte, Jakobs Sønner!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Han, HERREN, er vor Gud, hans Domme når ud over Jorden;
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 han ihukommer for evigt sin Pagt, i tusind Slægter sit Tilsagn,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Pagten, han slutted med Abraham, Eden, han tilsvor Isak;
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 han holdt den i Hævd som Ret for Jakob, en evig Pagt for Israel,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 idet han sagde: "Dig giver jeg Kana'ans Land som eders Arvelod."
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Da de kun var en liden Hob, kun få og fremmede der,
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 og vandrede fra Folk til Folk, fra et Rige til et andet,
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 tillod han ingen at volde dem Men, men tugted for deres Skyld Konger
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 "Rør ikke mine Salvede, gør ikke mine Profeter ondt!"
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Hungersnød kaldte han frem over Landet, hver Brødets Støttestav brød han;
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 han sendte forud for dem en Mand, Josef solgtes som Træl;
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 de tvang hans Fødder med Lænker, han kom i Lænker af Jern,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 indtil hans Ord blev opfyldt; ved HERRENs Ord stod han Prøven igennem.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 På Kongens Bud blev han fri, Folkenes Hersker lod ham løs:
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 han tog ham til Herre for sit Hus, til Hersker over alt sit Gods;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 han styred hans Øverster efter sin Vilje og viste hans Ældste til Rette.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Og Israel kom til Ægypten, Jakob boede som Gæst i Kamiternes Land.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Han lod sit Folk blive såre frugtbart og stærkere end dets Fjender;
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 han vendte deres Sind til Had mod sit Folk og til Træskhed imod sine Tjenere.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Da sendte han Moses, sin Tjener, og Aron, sin udvalgte Mand;
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 han gjorde sine Tegn i Ægypten og Undere i Kamiternes Land;
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 han sendte Mørke, så blev det mørkt, men de ænsede ikke hans Ord;
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 han gjorde deres Vande til Blod og slog deres Fisk ihjel;
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 af Frøer vrimlede Landet, selv i Kongens Sale var de;
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 han talede, så kom der Bremser og Myg i alt deres Land;
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 han sendte dem Hagl for Regn og luende Ild i Landet;
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 han slog både Vinstok og Figen og splintrede Træerne i deres Land;
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 han talede, så kom der Græshopper, Springere uden Tal,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 de åd alt Græs i Landet, de åd deres Jords Afgrøde;
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 alt førstefødt i Landet slog han, Førstegrøden af al deres Kraft;
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 han førte dem ud med Sølv og Guld, ikke een i hans Stammer snubled
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Ægypterne glæded sig, da de drog bort, thi de var grebet af Rædsel for dem.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Han bredte en Sky som Skjul og Ild til at lyse i Natten;
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 de krævede, han bragte Vagtler, med Himmelbrød mættede han dem;
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 han åbnede Klippen, og Vand strømmede ud, det løb som en Flod i Ørkenen.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Thi han kom sit hellige Ord i Hu til Abraham, sin Tjener;
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 han lod sit Folk drage ud med Fryd, sine udvalgte under Jubel;
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 han gav dem Folkenes Lande, de fik Folkeslags Gods i Eje.
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Derfor skulde de holde hans Bud og efterkomme hans Love. Halleluja!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Salme 105 >