< 4 Mosebog 17 >

1 Og HERREN talede til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 "Sig til Israelitterne, at Øversterne for Fædrenehusene skal give dig en Stav for hvert Fædrenehus, tolv Stave i alt, og skriv så hver enkelts Navn på hans Stav
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
3 og skriv Arons Navn på Levis Stav, thi hvert Overhoved for Fædrenehusene skal have een Stav.
A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
4 Læg dem så ind i Åbenbariogsteltet foran Vidnesbyrdet, der, hvor jeg åbenbarer mig for dig.
Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
5 Den Mand, jeg udvælger, hans Stav skal da grønnes; således vil jeg bringe Israelitternes Knurren imod eder til Tavshed, så jeg kan blive fri for den."
Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
6 Moses sagde nu dette til Israelitterne, og alle deres Øverster gav ham en Stav, så der blev en Stav for hver Øverste efter deres Fædrenehuse, tolv Stave i alt, og Arons Stav var imellem Stavene.
Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
7 Derpå lagde Moses Stavene hen foran HERRENs Åsyn i Vidnesbyrdets Telt.
Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
8 Da Moses næste Dag kom ind i Vidnesbyrdets Telt, se, da var Arons Stav, Staven for Levis Hus, grønnedes; den havde sat Skud, var kommet i Blomst og bar modne Mandler.
Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
9 Da tog Moses Stavene bort fra HERRENs Åsyn og bar dem ud til Israelitterne, og de så på dem og tog hver sin Stav.
Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
10 Men HERREN sagde til Moses: "Læg Arons Stav tilbage foran Vidnesbyrdet, for at den kan opbevares til Tegn for de genstridige, og gør Ende på deres Knurren, så jeg kan blive fri for den, at de ikke skal dø!"
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
11 Og Moses gjorde som HERREN havde pålagt ham; således gjorde han.
Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
12 Men Israelitterne sagde til Moses: "Se, vi omkommer, det er ude med os, det er ude med os alle sammen!
Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
13 Enhver, der kommer HERRENs Bolig nær, dør. Skal vi da virkelig omkomme alle sammen?"
Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”

< 4 Mosebog 17 >