< 4 Mosebog 14 >

1 Da opløftede hele Menigheden sin Røst og brød ud i Klageråb, og Folket græd Natten igennem.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 Og alle Israelitterne knurrede imod Moses og Aron, og hele Menigheden sagde til dem: "Gid vi var døde i Ægypten eller her i Ørkenen!
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 Hvorfor fører HERREN os til dette Land, når vi skal falde for Sværdet og vore Kvinder og Børn blive til Bytte? Var det dog ikke bedre for os at vende tilbage til Ægypten?"
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 Og de sagde til hverandre: "Lad os vælge os en Fører og vende tilbage til Ægypten!"
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Da faldt Moses og Aron på deres Ansigt foran hele den israelitiske Menigheds Forsamling.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 Men Josua, Nuns Søn, og Kaleb, Jefunnes Søn, der havde været med til at undersøge Landet, sønderrev deres Klæder
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 og sagde til hele Israelitternes Menighed: "Landet, vi har rejst igennem og undersøgt, er et såre, såre godt Land.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 Hvis HERREN har Behag i os, vil han føre os til det Land og give os det, et Land, der flyder med Mælk og Honning.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Gør kun ikke Oprør imod HERREN og frygt ikke for Landets Befolkning, thi dem tager vi som en Bid Brød; deres Skygge er veget fra dem, men med os er HERREN; frygt ikke for dem!"
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 Hele Menigheden tænkte allerede på at stene dem; men da kom HERRENs Herlighed til Syne for alle Israelitterne ved Åbenbaringsteltet.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 Og HERREN sagde til Moses: "Hvor længe skal dette Folk håne mig, og hvor længe vil det vægre sig ved at tro på mig, til Trods for alle de Tegn jeg har gjort i det?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 Jeg vil slå det med Pest og udrydde det, men dig vil jeg gøre til et Folk, større og stærkere end det!"
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 Men Moses sagde til HERREN: "Ægypterne har hørt, at du i din Vælde har ført dette Folk bort fra dem;
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 og ligeledes har alle dette Lands Indbyggere hørt, at du, HERRE, er midt iblandt dette Folk, thi du, HERRE, åbenbarer dig synligt, idet din Sky står over dem, og du vandrer foran dem om Dagen i en Skystøtte og om Natten i en Ildstøtte.
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 Hvis du nu dræber dette Folk alle som een, vil de Folk, der har hørt dit Ry, sige:
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 Fordi HERREN ikke evnede at føre dette Folk til det Land, han havde tilsvoret dem, lod han dem omkomme i Ørkenen.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 Derfor, HERRE, lad din Vælde nu vise sig i sin Storhed, således som du forjættede, da du sagde:
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 HERREN er langmodig og rig på Miskundhed, han forlader Misgerning og Overtrædelse, men han lader ingen ustraffet, og han hjemsøger Fædrenes Brøde på Børnene i tredje og fjerde Led.
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Så tilgiv nu dette Folk dets Misgerning efter din store Miskundhed, således som du har tilgivet dette Folk hele Vejen fra Ægypten og hertil!"
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 Da sagde HERREN: "Jeg tilgiver dem på din Bøn.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Men så sandt jeg lever så sandt hele Jorden skal opfyldes af HERRENs Herlighed:
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 Ingen af de Mænd, der har set min Herlighed og de Tegn, jeg har gjort i Ægypten og i Ørkenen, og dog nu for tiende Gang har fristet mig og ikke villet lyde min Røst,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 ingen af dem skal se det Land, jeg tilsvor deres Fædre! Ingen af dem, der har hånet mig, skal få det at se;
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 kun min Tjener Kaleb lader jeg komme til det Land, han har været i, og hans Efterkommere skal få det i Eje, fordi han havde en anden Ånd og viste mig fuld Lydighed.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 Men Amalekiterne og Kana'anæerne bor i Lavlandet. Vend derfor om i Morgen, bryd op og drag ud i Ørkenen ad det røde Hav til!"
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 Fremdeles talede HERREN til Moses og Aron og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 "Hvor længe skal jeg tåle denne onde Menighed, dem, som bestandig knurrer imod mig? Jeg har hørt Israelitternes Knurren, hørt, hvorledes de knurrer imod mig.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Sig til dem: Så sandt jeg lever lyder det fra HERREN, som I har råbt mig i Øret, således vil jeg handle med eder!
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 I Ørkenen her skal eders Kroppe falde, alle I, der blev mønstret, så mange I er fra Tyveårsalderen og opefter, I, som har knurret imod mig.
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 Sandelig, ingen af eder skal komme til det Land, jeg med løftet Hånd svor at ville giver eder at bo i, med Undtagelse af Kaleb, Jefunnes Søn, og Josua, Nuns Søn.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 Eders små Børn, som I sagde vilde blive til Bytte, dem vil jeg lade komme derhen, og de skal tage det Land i Besiddelse, som I har vraget,
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 men eders egne Kroppe skal falde i Ørkenen her,
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 og eders Sønner skal flakke om i Ørkenen i fyrretyve År og undgælde for eders Bolen, indtil eders Kroppe er gået til Grunde i Ørkenen.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 Som I brugte fyrretyve Dage til at undersøge Landet, således skal I undgælde for eders Misgerninger i fyrretyve År, eet År for hver Dag, og således få mit Mishag at føle.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 Jeg HERREN har sagt det: Sandelig, således vil jeg handle med hele denne onde Menighed, der har rottet sig sammen imod mig; i Ørkenen her skal de gå til Grunde, i den skal de dø!"
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 Og de Mænd, Moses havde udsendt for at undersøge Landet, og som efter deres Tilbagekomst havde fået hele Menigheden til at knurre imod ham ved at tale nedsættende om Landet,
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 de Mænd, der havde talt nedsættende om Landet, fik en brat Død for HERRENs Åsyn:
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 kun Josua, Nuns Søn, og Kaleb, Jefunnes Søn, blev i Live af de Mænd, der var draget hen for at undersøge Landet.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 Men da Moses forebragte alle Israelitterne disse Ord, grebes Folket af stor Sorg;
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 og tidligt næste Morgen drog de op mod det øverste af Bjerglandet og sagde: "Se, vi er rede til at drage op til det Sted, HERREN har talet om, thi vi, har syndet."
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 Da sagde Moses: "Hvorfor vil I overtræde HERRENs Bud? Det vil ikke gå godt!
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Drag ikke derop, thi HERREN er ikke iblandt eder; gør I det, bliver I slået af eders Fjender!
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 Thi Amalekiterne og Kana'anæerne vil møde eder der, og I skal falde for Sværdet; I har jo vendt eder fra HERREN, og HERREN er ikke med eder!"
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Alligevel formastede de sig til at drage op mod det øverste af Bjerglandet; men HERRENs Pagts Ark og Moses forlod ikke Lejren.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Da steg Amalekiterne og Kana'anæerne, der boede der i Bjerglandet, ned og slog dem og adsplittede dem lige til Horma.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.

< 4 Mosebog 14 >