< Nehemias 2 >
1 I Nisan Måned i Kong Artaxerxes's tyvende Regeringsår, da jeg skulde sørge for Vin, har jeg engang Vinen frem og rakte Kongen den. Jeg havde ikke før set modfalden ud, når jeg stod for hans Ansigt.
A watan Nisan a shekara ta ashirin ta mulkin Sarki Artazerzes, sa’ad aka kawo masa ruwan inabi, sai na karɓa na ba shi. Ban taɓa ɓata fuskata a gabansa ba, sai wannan karo.
2 Og Kongen sagde til mig: Hvorfor ser du så modfalden ud? Du er jo ikke syg; det kan ikke være andet, end at du har en Hjertesorg! Da blev jeg såre bange,
Saboda haka sarki ya tambaye ni ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake ba? Ba abin da ya kawo wannan, in ba dai kana baƙin ciki ba.” Sai na ji tsoro ƙwarai,
3 og jeg sagde til Kongen: "Kongen leve evindelig! Hvor kan jeg andet end se modfalden ud, når den By, hvor mine Fædres Grave er, ligger øde, og dens Porte er fortæret af Ilden?
na amsa na ce wa sarki, “Ran sarki yă daɗe! Me zai hana fuskata ta ɓaci, sa’ad da birnin da aka binne kakannina tana zaman kango, aka kuma rushe ƙofofinsa da wuta?”
4 Kongen spurgte mig da: "Hvad er det, du ønsker? Så bad jeg til Himmelens Gud,"
Sai sarki ya ce mini, “Me kake so?” Sai na yi addu’a ga Allah na sama,
5 og jeg sagde til Kongen: "Hvis Kongen synes, og hvis din Tjener er dig til Behag, beder jeg om, at du vil lade mig rejse til Juda, til den By, hvor mine Fædres Grave er, og lade mig bygge den op igen!
na kuwa ba wa sarki amsa, na ce, “In ya gamshi sarki, in kuma bawanka ya sami tagomashi a idonka, bari ka aike ni in tafi ƙasar Yahuda, birnin da aka binne kakannina, domin in sāke gina shi.”
6 Da sagde Kongen til mig, medens Dronningen sad ved hans Side: "Hvor længe vil den Rejse vare, og hvornår kan du vende tilbage? Og da Kongen således fandt for godt at lade mig rejse, opgav jeg ham en Tid.
Sai sarki, a lokacin sarauniya da tana zama kusa da shi, ya tambaye ni, ya ce, “Kwana nawa tafiyar za tă ɗauke ka, kuma yaushe za ka dawo?” Ya gamshi sarki ya aike ni; saboda haka na shirya lokaci.
7 Og jeg sagde til Kongen: Hvis Kongen synes, så lad mig få Breve med til Statholderne hinsides Floden, så de lader mig drage videre, til jeg når Juda,
Na kuma ce masa, “In ya gamshi sarki, zai yi kyau in sami wasiƙu zuwa ga gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, domin su tanada kāriya har sai na isa Yahuda?
8 og et Brev til Asaf, Opsynsmanden. over den kongelige Skov, at han skal give mig Træ til Bjælkeværket i Tempelborgens Porte og til Byens Mur og det Hus, jeg tager ind i! Det gav Kongen mig, eftersom min Guds gode Hånd var over mig.
A kuma ba ni wasiƙa zuwa ga Asaf, sarkin daji, yă ba ni katako don yin ƙofofin kagara na kusa da fadar haikali da kuma don katangar birni, da na wurin da zan zauna?” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.
9 Da jeg kom til Statholderne hinsides Floden, gav jeg dem Kongens Breve; desuden havde Kongen givet mig Hærførere og Ryttere med på Rejsen.
Saboda haka na tafi wurin gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, na ba su wasiƙun sarki. Sarki kuma ya aika da hafsoshin mayaƙa da kuma mahayan dawakai tare da ni.
10 Men da Horoniten Sanballat og den ammonitiske Træl Tobija hørte det, ærgrede de sig højligen over, at der var kommet en Mand for at arbejde på Israeliternes Bedste.
Da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon suka ji cewa wani ya zo domin yă ƙarfafa zaman lafiyar mutanen Isra’ila, sai suka damu ƙwarai.
11 Så kom jeg til Jerusalem, og da jeg havde været der i tre Dage,
Sai na je Urushalima, bayan na zauna a can na kwanaki uku,
12 brød jeg op ved Nattetide sammen med nogle få Mænd uden at have sagt noget Menneske, hvad min Gud havde skudt mig i Sinde at gøre for Jerusalem; og der var intet andet Dyr med end det, jeg red på.
sai na fita da dare tare da mutane kalila. Ban faɗa wa wani abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi don Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.
13 Jeg red så om Natten ud gennem Dalporten i Retning af Dragekilden og hen til Møgporten, idet jeg undersøgte Jerusalems Mure, der var nedrevet, og Portene, der var fortæret af Ilden;
Da dare na fita ta Ƙofar Kwari wajen Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, ina dudduba katangar Urushalima waɗanda aka rushe da kuma ƙofofinta waɗanda aka ƙone da wuta.
14 derpå red jeg videre til Kildeporten og Kongedammen, men der var ikke Plads nok til, at mit Ridedyr kunde komme frem med mig.
Sa’an nan na ci gaba zuwa wajen Ƙofar Maɓuɓɓuga da kuma Tafkin Sarki, amma babu isashen wuri saboda abin da na hau yă bi;
15 Så red jeg om Natten op igennem Dalen og undersøgte Muren, forandrede Retning og red så ind igennem Dalporten, hvorpå jeg vendte hjem.
saboda haka na haura ta kwarin da dad dare, ina dudduba katangar. A ƙarshe, na juya na sāke shiga ta Ƙofar Kwari.
16 Forstanderne vidste ikke, hvor jeg var gået hen, eller hvad jeg foretog mig; og hverken Jøderne, Præsterne, Stormændene, Forstanderne eller de andre, der skulde have med Arbejdet at gøre, havde jeg endnu sagt noget.
Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da nake yi ba, domin ban riga na faɗa wa Yahudawa, ko firistoci, ko manyan gari, ko shugabanni, ko sauran waɗanda za su yi aiki, kome ba.
17 Men nu sagde jeg til dem: I ser den Ulykke, vi er i, hvorledes Jerusalem er ødelagt og Portene opbrændt; kom derforog lad os opbygge Jerusalems Mur, så vi ikke mere skal være til Spot!
Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”
18 Og da jeg fortalte dem, hvorledes min Guds gode Hånd havde været over mig, og om de Ord, Kongen havde talt til mig, sagde de: Lad os gøre os rede og bygge! Og de tog sig sammen til det gode Værk.
Na kuma faɗa musu game da yadda alherin Allahna yake tare da ni da kuma abin da sarki ya faɗa mini. Suka amsa, suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Sai suka fara wannan aiki mai kyau.
19 Da Horoniten Sanballat, den ammonitiske Træl Tobija og Araberen Gesjem hørte det, spottede de os og sagde hånligt til os: Hvad er det, I der har for? Sætter I eder op mod Kongen?
Amma sa’ad da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon da kuma Geshem mutumin Arab suka ji game da wannan, sai suka yi mana ba’a suka kuma yi mana dariya. Suka ce, “Me kuke tsammani kuke yi? Kuna so ku yi wa sarki tawaye ne?”
20 Men jeg gav dem til Svar: "Himmelens Gud vil lade det lykkes for os, og vi, hans Tjenere, vil gøre os rede og bygge; men I har ingen Del eller Ret eller Ihukommelse i Jerusalem!"
Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”