< Matthæus 27 >

1 Men da det var blevet Morgen, holdt alle Ypperstepræsterne og Folkets Ældste Råd imod Jesus for at aflive ham.
Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
2 Og de bandt ham og førte ham bort og overgave ham til Landshøvdingen Pontius Pilatus.
Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
3 Da nu Judas, som forrådte ham, så, at han var bleven domfældt, fortrød han det og bragte de tredive Sølvpenge tilbage til Ypperstepræsterne og de Ældste og sagde:
Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
4 "Jeg har syndet, idet jeg forrådte uskyldigt Blod." Men de sagde: "Hvad kommer det os ved? se du dertil."
Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
5 Og han kastede Sølvpengene ind i Templet, veg bort og gik hen og hængte sig.
Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
6 Men Ypperstepræsterne toge Sølvpengene og sagde: "Det er ikke tilladt at lægge dem til Tempelskatten; thi det er Blodpenge."
Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
7 Men efter at have holdt Råd købte de Pottemagermarken derfor til Gravsted for de fremmede.
Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
8 Derfor blev den Mark kaldt Blodmarken indtil den Dag i Dag.
Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
9 Da opfyldtes det, som er talt ved Profeten Jeremias, som siger: "Og de toge de tredive Sølvpenge, Prisen for den vurderede, hvem de vurderede for Israels Børn,
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
10 og de gav dem for Pottemagermarken, som Herren befalede mig."
suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 Men Jesus blev stillet for Landshøvdingen, og Landshøvdingen spurgte ham og sagde: "Er du Jødernes Konge?" Men Jesus sagde til ham: "Du siger det."
Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
12 Og da han blev anklaget af Ypperstepræsterne og de Ældste, svarede han intet.
Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
13 Da siger Pilatus til ham: "Hører du ikke, hvor meget de vidne imod dig?"
Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
14 Og han svarede ham end ikke på et eneste Ord, så at Landshøvdingen undrede sig såre.
Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
15 Men på Højtiden plejede Landshøvdingen at løslade Mængden een Fange, hvilken de vilde.
A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
16 Og de havde dengang en berygtet Fange, som hed Barabbas.
To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
17 Da de vare forsamlede, sagde Pilatus derfor til dem: "Hvem ville I, at jeg skal løslade eder: Barabbas eller Jesus, som kaldes Kristus?"
Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
18 Thi han vidste, at det var af Avind, de havde overgivet ham.
Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
19 Men medens han sad på Dommersædet, sendte hans Hustru Bud til ham og sagde: "Befat dig ikke med denne retfærdige; thi jeg har lidt meget i Dag i en Drøm før hans Skyld."
Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
20 Men Ypperstepræsterne og de Ældste overtalte Skarerne til, at de skulde begære Barabbas, men ihjelslå Jesus.
Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
21 Og Landshøvdingen svarede og sagde til dem: "Hvilken af de to ville I, at jeg skal løslade eder?" Men de sagde: "Barabas."
Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
22 Pilatus siger til dem: "Hvad skal jeg da gøre med Jesus, som kaldes Kristus?" De sige alle: "Lad ham blive korsfæstet!"
Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
23 Men Landshøvdingen sagde: "Hvad ondt har han da gjort?" Men de råbte end mere og sagde: "Lad ham blive korsfæstet!"
Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
24 Men da Pilatus så, at han intet udrettede, men at der blev større Larm, tog han Vand og toede sine Hænder i Mængdens Påsyn og sagde: "Jeg er uskyldig i denne retfærdiges Blod; ser I dertil!"
Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
25 Og hele Folket svarede og sagde: "Hans Blod komme over os og over vore Børn!"
Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
26 Da løslod han dem Barabbas; men Jesus lod han hudstryge og gav ham hen til at korsfæstes.
Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
27 Da toge Landshøvdingens Stridsmænd Jesus med sig ind i Borgen og samlede hele Vagtafdelingen omkring ham.
Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
28 Og de afklædte ham og kastede en Skarlagens Kappe om ham.
Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
29 Og de flettede en Krone af Torne og satte den på hans Hoved og gave ham et Rør i hans højre Hånd; og de faldt på Knæ for ham og spottede ham og sagde: "Hil være dig, du Jødernes Konge!"
Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
30 Og de spyttede på ham og toge Røret og sloge ham på Hovedet.
Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
31 Og da de havde spottet ham, toge de Kappen af ham og iførte ham hans egne Klæder og førte ham hen for at korsfæste ham.
Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
32 Men medens de gik derud, traf de en Mand fra Kyrene, ved Navn Simon; ham tvang de til at bære hans Kors.
Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
33 Og da de kom til et Sted, som kaldes Golgatha, det er udlagt: "Hovedskalsted",
Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
34 gave de ham Eddike at drikke blandet med Galde og da han smagte det, vilde han ikke drikke.
A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
35 Men da de havde korsfæstet ham, delte de hans Klæder imellem sig ved Lodkastning, for at det skulde opfyldes, som er sagt af Profeten: "De delte mine Klæder imellem sig og kastede Lod om mit Klædebon."
Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
36 Og de sade der og holdt Vagt over ham.
Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
37 Og oven over hans Hoved satte de Beskyldningen imod ham skreven således: "Dette er Jesus, Jødernes Konge."
Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
38 Da bliver der korsfæstet to Røvere sammen med ham, en ved den højre og en ved den venstre Side,
An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
39 Og de, som gik forbi, spottede ham, idet de rystede på deres Hoveder og sagde:
Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
40 "Du, som nedbryder Templet og bygger det op i tre Dage, frels dig selv; er du Guds Søn, da stig ned af Korset!"
suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
41 "Ligeså spottede Ypperstepræsterne tillige med de skriftkloge og de Ældste og sagde:
Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
42 "Andre har han frelst, sig selv kan han ikke frelse; er han Israels Konge, så lad ham nu stige ned af Korset, så ville vi tro på ham.
“Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
43 Han har sat sin Lid til Gud; han fri ham nu, om han har Behag i ham; thi han har sagt: Jeg er Guds Søn."
Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
44 Og på samme Måde hånede også Røverne ham, som vare korsfæstede med ham.
Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
45 Men fra den sjette Time blev der Mørke over hele Landet indtil den niende Time.
Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
46 Og ved den niende Time råbte Jesus med høj Røst og sagde: "Eli! Eli! Lama Sabaktani?" det er: "Min Gud! min Gud! hvorfor har du forladt mig?"
Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
47 Men nogle af dem, som stode der og hørte det, sagde: "Han kalder på Elias."
Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
48 Og straks løb en af dem hen og tog en Svamp og fyldte den med Eddike og stak den på et Rør og gav ham at drikke.
Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
49 Men de andre sagde: "Holdt! lader os se, om Elias kommer for at frelse ham."
Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
50 Men Jesus råbte atter med høj Røst og opgav Ånden.
Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
51 Og se, Forhænget i Templet splittedes i to Stykker, fra øverst til nederst; og Jorden skjalv, og Klipperne revnede,
A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
52 og Gravene åbnedes; og mange af de hensovede helliges legemer bleve oprejste,
Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
53 og de gik ud af Gravene efter hans Opstandelse og kom ind i den hellige Stad og viste sig for mange.
Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Men da Høvedsmanden og de, som tillige med, ham holdt Vagt over Jesus, så Jordskælvet, og hvad der skete, frygtede de såre og sagde: "Sandelig, denne var Guds Søn."
Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
55 Men der var mange Kvinder der, som så til i Frastand, hvilke havde fulgt Jesus fra Galilæa og tjent ham.
Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
56 Iblandt dem vare Maria Magdalene og Maria, Jakobs og Josefs Moder, og Zebedæus's Sønners Moder.
A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
57 Men da det var blevet Aften, kom en rig Mand fra Arimathæa, ved Navn Josef, som også selv var bleven Jesu Discipel.
Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
58 Han gik til Pilatus og bad om Jesu Legeme. Da befalede Pilatus, at det skulde udleveres.
Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
59 Og Josef tog Legemet og svøbte det i et rent, fint Linklæde
Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
60 og lagde det i sin nye Grav, som han havde ladet hugge i Klippen, og væltede en stor Sten for Indgangen til Graven og gik bort.
Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
61 Men Maria Magdalene og den anden Maria vare der, og de sade lige over for Graven.
Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
62 Men den næste Dag, som var Dagen efter Beredelsesdagen, forsamlede Ypperstepræsterne og Farisæerne sig hos Pilatus
Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
63 og sagde: "Herre! vi ere komne i Hu, at denne Forfører sagde, medens han endnu levede: Tre Dage efter bliver jeg oprejst.
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
64 Befal derfor, at Graven skal sikkert bevogtes indtil den tredje Dag, for at ikke hans Disciple skulle komme og stjæle ham og sige til Folket: "Han er oprejst fra de døde; og da vil den sidste Forførelse blive værre end den første,"
Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
65 Pilatus sagde til dem: "Der have I en Vagt; går hen og bevogter den sikkert, som I bedst vide!"
Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
66 Og de gik hen og bevogtede Graven sikkert med Vagten efter at have sat Segl for Stenen.
Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.

< Matthæus 27 >