< Matthæus 26 >

1 Og det skete, da Jesus havde fuldendt alle disse Ord, sagde han til sine Disciple:
Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa,
2 "I vide, at om to Dage er det Påske; så forrådes Menneskesønnen til at korsfæstes."
“Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.
3 Da forsamledes Ypperstepræsterne og Folkets Ældste i Ypperstepræstens Gård; han hed Kajfas.
Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa.
4 Og de rådsloge om at gribe Jesus med List og ihjelslå ham.
Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi.
5 Men de sagde: "Ikke på Højtiden, for at der ikke skal blive Oprør iblandt Folket."
Amma suna cewa, “Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane.”
6 Men da Jesus var kommen til Bethania, i Simon den spedalskes Hus,
Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu,
7 kom der en Kvinde til ham, som havde en Alabastkrukke med såre kostbar Salve, og hun udgød den på hans Hoved, medens han sad til Bords.
daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa.
8 Men da Disciplene så det, bleve de vrede og sagde: "Hvortil denne Spilde?
Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Ina dalilin yin irin wannan asara?
9 Dette kunde jo være solgt til en høj Pris og være givet til fattige."
Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa.”
10 Men da Jesus mærkede det, sagde han til dem: "Hvorfor volde I Kvinden Fortrædeligheder? Hun har jo gjort en god Gerning imod mig.
Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, “Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina.
11 Thi de fattige have I altid hos eder; men mig have I ikke altid.
Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.
12 Thi da hun udgød denne Salve over mit Legeme, gjorde hun det for at berede mig til at begraves.
Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta.
13 Sandelig, siger jeg eder, hvor som helst i hele Verden dette Evangelium bliver prædiket, skal også det, som hun har gjort, omtales til hendes Ihukommelse."
Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita.”
14 Da gik en af de tolv, han, som hed Judas Iskariot, hen til Ypperstepræsterne
Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin,
15 og sagde: "Hvad ville I give mig, så skal jeg forråde ham til eder?" Men de betalte ham tredive Sølvpenge".
yace, ''Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?” Suka auna masa azurfa talatin.
16 Og fra den Stund søgte han Lejlighed til at forråde ham.
Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.
17 Men på den første Dag af de usyrede Brøds Højtid kom Disciplene til Jesus og sagde: "Hvor vil du, at vi skulle træffe Forberedelse for dig til at spise Påskelammet?"
To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?”
18 Men han sagde: "Går ind i Staden til den og den Mand, og siger til ham: Mesteren siger: Min Time er nær; hos dig holder jeg Påske med mine Disciple."
Yace, “Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, “lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina.”'''
19 Og Disciplene gjorde, som Jesus befalede dem, og beredte Påskelammet.
Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.
20 Men da det var blevet Aften, sad han til Bords med de tolv.
Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu.
21 Og medens de spiste, sagde han: "Sandelig, siger jeg eder, en af eder vil forråde mig."
Sa'adda suke ci, yace, “Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni.”
22 Og de bleve såre bedrøvede og begyndte hver især at sige til ham: "Det er dog vel ikke mig, Herre?"
Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, ''Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?”
23 Men han svarede og sagde: "Den, som dyppede Hånden tillige med mig i Fadet, han vil forråde mig.
Sai ya amsa, “Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni.
24 Menneskesønnen går vel bort, som der er skrevet om ham; men ve det Menneske, ved hvem Menneskesønnen bliver forrådt! Det var godt for det Menneske, om han ikke var født."
Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba.”
25 Men Judas, som forrådte ham, svarede og sagde: "Det er dog vel ikke mig, Rabbi?" Han siger til ham: "Du har sagt det."
Yahuza da zai bada shi yace, “Mallam ko ni ne?” Yace masa, “Ka fada da kanka.”
26 Men medens de spiste, tog Jesus Brød, og han velsignede og brød det og gav Disciplene det og sagde: "Tager, æder; dette er mit Legeme."
Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, “Ku karba, ku ci, wannan jiki nane.”
27 Og han tog en Kalk og takkede. gav dem den og sagde: "Drikker alle deraf;
Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, “Ku sha, dukanku.
28 thi dette er mit Blod, Pagtens, hvilket udgydes for mange til Syndernes Forladelse.
“Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa.
29 Men jeg siger eder, fra nu af skal jeg ingenlunde drikke af denne Vintræets Frugt indtil den Dag, da jeg skal drikke den ny med eder i min Faders Rige."
Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana.”
30 Og da de havde sunget Lovsangen, gik de ud til Oliebjerget.
Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun.
31 Da siger Jesus til dem: "I skulle alle forarges på mig i denne Nat; thi der er skrevet: Jeg vil slå Hyrden, og Hjordens Får skulle adspredes.
Sai Yesu yace masu, “Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, ''Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.'
32 Men efter at jeg er bleven oprejst, vil jeg gå forud for eder til Galilæa."
Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili.”
33 Men Peter svarede og sagde til ham: "Om end alle ville forarges på dig, så vil jeg dog aldrig forarges."
Amma Bitrus yace masa, “Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba.”
34 Jesus sagde til ham: "Sandelig, siger jeg dig, i denne Nat, førend Hanen galer, skal du fornægte mig tre Gange."
Yesu yace masa, ''Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku.”
35 Peter siger til ham: "Om jeg end skulde dø med dig, vil jeg ingenlunde fornægte dig." Ligeså sagde også alle Disciplene.
Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba.” Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.
36 Da kommer Jesus med dem til en Gård, som kaldes Gethsemane, og han siger til Disciplene: "Sætter eder her, medens jeg går derhen og beder."
Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, ''Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a.”
37 Og han tog Peter og Zebedæus's to Sønner med sig, og han begyndte at bedrøves og svarlig at ængstes.
Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi.
38 Da siger han til dem: "Min Sjæl er dybt bedrøvet indtil Døden; bliver her og våger med mig!"
Sai yace masu, “Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni.”
39 Og han gik lidt frem, faldt på sit Ansigt, bad og sagde: "Min Fader! er det muligt, da gå denne Kalk mig forbi; dog ikke som jeg vil, men som du vil."
Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, “Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin.”
40 Og han kommer til Disciplene og finder dem sovende, og han siger til Peter: "Så kunde I da ikke våge een Time med mig!
Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, “Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya?
41 Våger og beder, for at I ikke skulle falde i Fristelse! Ånden er vel redebon, men Kødet er skrøbeligt."
Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi.”
42 Han gik atter anden Gang hen, bad og sagde: "Min Fader! hvis denne Kalk ikke kan gå mig forbi, uden jeg drikker den, da ske din Villie!"
Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, “Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance.”
43 Og han kom og fandt dem atter sovende, thi deres Øjne vare betyngede.
Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi.
44 Og han forlod dem og gik atter hen og bad tredje Gang og sagde atter det samme Ord.
Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.
45 Da kommer han til Disciplene og siger til dem: "Sove I fremdeles og Hvile eder? Se, Timen er nær, og Menneskesønnen forrådes i Synderes Hænder.
Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, “Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi.
46 Står op, lader os gå; se, han, som forråder mig, er nær."
Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato.”
47 Og medens han endnu talte, se, da kom Judas, en af de tolv, og med ham en stor Skare, med Sværd og Knipler, fra Ypperstepræsterne og Folkets Ældste.
Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake.
48 Men han, som forrådte ham, havde givet dem et Tegn og sagt: "Den, som jeg kysser, ham er det; griber ham!"
To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, ''Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi.''
49 Og han trådte straks hen til Jesus og sagde: "Hil være dig, Rabbi!" og kyssede ham.
Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, “Gaisuwa, Mallam!” sai ya sumbace shi.
50 Men Jesus sagde til ham: "Ven, hvorfor kommer du her?" Da trådte de til og lagde Hånd på Jesus og grebe ham.
Yesu kuwa yace masa, “Aboki, kayi abin da ya kawo ka.” Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.
51 Og se, en af dem, som vare med Jesus, rakte Hånden ud og drog sit Sværd og slog Ypperstepræstens Tjener og huggede hans Øre af.
Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne.
52 Da siger Jesus til ham: "Stik dit Sværd igen på dets Sted; thi alle de, som tage Sværd, skulle omkomme ved Sværd.
Sai Yesu yace, masa, “Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka.
53 Eller mener du, at jeg ikke kan bede min Fader, så han nu tilskikker mig mere end tolv Legioner Engle?
Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu?
54 Hvorledes skulde da Skrifterne opfyldes, at det bør gå således til?"
Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?''
55 I den samme Time sagde Jesus til Skarerne: "I ere gåede ud ligesom imod en Røver med Sværd og Knipler for at fange mig. Daglig sad jeg i Helligdommen og lærte, og I grebe mig ikke.
A wannan lokacin Yesu yace wa taron, “Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba.
56 Men det er alt sammen sket, for at Profeternes Skrifter skulde opfyldes." Da forlode alle Disciplene ham og flyede.
Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta.” Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.
57 Men de, som havde grebet Jesus, førte ham hen til Ypperstepræsten Kajfas, hvor de skriftkloge og de Ældste vare forsamlede.
Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru.
58 Men Peter fulgte ham i Frastand indtil Ypperstepræstens Gård, og han gik indenfor og satte sig hos Svendene for at se, hvad Udgang det vilde få.
Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.
59 Men Ypperstepræsterne og hele Rådet søgte falsk Vidnesbyrd imod Jesus, for at de kunde aflive ham.
A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi.
60 Og de fandt intet, endskønt der trådte mange falske Vidner frem. Men til sidst trådte to frem og sagde:
Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito
61 "Denne har sagt: Jeg kan nedbryde Guds Tempel og bygge det op i tre Dage."
sukace ''Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'''
62 Og Ypperstepræsten stod op og sagde til ham: "Svarer du intet på, hvad disse vidne imod dig?"
Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, “Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?”
63 Men Jesus tav. Og Ypperstepræsten tog til Orde og sagde til ham: "Jeg besværger dig ved den levende Gud, at du siger os, om du er Kristus, Guds Søn."
Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, “Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah.''
64 Jesus siger til ham: "Du har sagt det; dog jeg siger eder: Fra nu af skulle I se Menneskesønnen sidde ved Kraftens højre Hånd og komme på Himmelens Skyer."
Yesu ya amsa masa, “Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama.”
65 Da sønderrev Ypperstepræsten sine Klæder og sagde: "Han har talt bespotteligt; hvad have vi længere Vidner nødig? se, nu have I hørt Bespottelsen.
Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, “Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon.
66 Hvad tykkes eder?" Og de svarede og sagde: "Han er skyldig til Døden."
Menene tunaninku?” Suka amsa sukace, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Da spyttede de ham i Ansigtet og gave ham Næveslag; andre sloge ham på Kinden
Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu,
68 og sagde: "Profeter os, Kristus, hvem var det, der slog dig?"
sukace, ''Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.
69 Men Peter sad udenfor i Gården; og en Pige kom hen til ham og sagde: "Også du var med Jesus Galilæeren."
To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, “Kaima kana tare da Yesu na Galili.”
70 Men han nægtede det i alles Påhør og sagde: "Jeg forstår ikke, hvad du siger."
Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, “Ban ma san abinda kike magana akai ba.”
71 Men da han gik ud i Portrummet, så en anden Pige ham; og hun siger til dem, som vare der: "Denne var med Jesus af Nazareth."
Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, “Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 Og han nægtede det atter med en Ed: "Jeg kender ikke det Menneske."
Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, “Ban san mutumin nan ba.”
73 Men lidt efter kom de, som stode der, hen og sagde til Peter: "Sandelig, også du er en af dem. dit Mål røber dig jo også."
Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, “Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka.”
74 Da begyndte han at forbande sig og sværge: "Jeg kender ikke det Menneske." Og straks galede Hanen.
Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, ''Ban san wannan mutumin ba,” nan da nan zakara yayi cara.
75 Og Peter kom Jesu Ord i Hu at han havde sagt: "Førend Hanen galer, skal du fornægte mig tre Gange." Og han gik udenfor og græd bitterligt.
Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, “Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku.” Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi.''

< Matthæus 26 >