< Matthæus 24 >

1 Og Jesus gik ud, bort fra Helligdommen, og hans Disciple kom til ham for at vise ham Helligdommens Bygninger.
Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
2 Men han svarede og sagde til dem: "Se I ikke alt dette? Sandelig, siger jeg eder, her skal ikke lades Sten på Sten, som jo skal nedbrydes."
Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
3 Men da han sad på Oliebjerget, kom hans Disciple til ham afsides og sagde: "Sig os, når skal dette ske? Og hvad er Tegnet på din Tilkommelse og Verdens Ende?" (aiōn g165)
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
4 Og Jesus svarede og sagde til dem: "Ser til, at ingen forfører eder!
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5 Thi mange skulle på mit Navn komme og sige: Jeg er Kristus; og de skulle forføre mange.
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6 Men I skulle få at høre om Krige og Krigsrygter. Ser til, lader eder ikke forskrække; thi det må ske; men Enden er ikke endda.
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7 Thi Folk skal rejse sig mod Folk, og Rige mod Rige, og der skal være Hungersnød og Jordskælv her og der.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8 Men alt dette er Veernes Begyndelse.
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9 Da skulle de overgive eder til Trængsel og slå eder ihjel, og I skulle hades af alle Folkeslagene for mit Navns Skyld.
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10 Og da skulle mange forarges og forråde hverandre og hade hverandre.
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11 Og mange falske Profeter skulle fremstå og forføre mange.
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
12 Og fordi Lovløsheden bliver mangfoldig, vil Kærligheden blive kold hos de fleste.
Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
13 Men den, som holder ud indtil Enden, han skal frelses.
amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 Og dette Rigets Evangelium skal prædikes i hele Verden til et Vidnesbyrd for alle Folkeslagene; og da skal Enden komme.
Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
15 Når I da se Ødelæggelsens Vederstyggelighed, hvorom der er talt ved Profeten Daniel, stå på hellig Grund, (den, som læser det, han give Agt!)
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16 da skulle de, som ere i Judæa, fly ud på Bjergene;
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17 den, som er på Taget, stige ikke ned for at hente, hvad der er i hans Hus;
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18 og den, som er på Marken, vende ikke tilbage før at hente sine Klæder!
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19 Men ve de frugtsommelige og dem, som give Die, i de Dage!
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20 Og beder om, at eders Flugt ikke skal ske om Vinteren, ej heller på en Sabbat;
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21 thi der skal da være en Trængsel så stor, som der ikke har været fra Verdens Begyndelse indtil nu og heller ikke skal komme.
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22 Og dersom disse Dage ikke bleve afkortede, da blev intet Kød frelst; men for de udvalgtes Skyld skulle disse Dage afkortes.
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23 Dersom nogen da siger til eder: Se, her er Kristus, eller der! da skulle I ikke tro det.
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24 Thi falske Krister og falske Profeter skulle fremstå og gøre store Tegn og Undergerninger, så at også de udvalgte skulde blive forførte, om det var muligt.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
25 Se, jeg har sagt eder det forud.
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26 Derfor, om de sige til eder: Se, han er i Ørkenen, da går ikke derud; se. han er i Kamrene, da tror det ikke!
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27 Thi ligesom Lynet udgår fra Østen og lyser indtil Vesten, således skal Menneskesønnens Tilkommelse være.
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28 Hvor Ådselet er, der ville Ørnene samle sig.
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
29 Men straks efter de Dages Trængsel skal Solen formørkes og Månen ikke give sit Skin og Stjernerne falde ned fra Himmelen, og Himmelens Kræfter skulle rystes.
“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
30 Og da skal Menneskesønnens Tegn vise sig på Himmelen; og da skulle alle Jordens Stammer jamre sig, og de skulle se Menneskesønnen komme på Himmelens Skyer med Kraft og megen Herlighed.
“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
31 Og han skal udsende sine Engle med stærktlydende Basun, og de skulle samle hans udvalgte fra de fire Vinde, fra den ene Ende af Himmelen til den anden.
Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
32 Men lærer Lignelsen af Figentræet: Når dets Gren allerede er bleven blød, og Bladene skyde frem, da skønne I, at Sommeren er nær.
“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
33 Således skulle også I, når I se alt dette, skønne, at han er nær for Døren.
Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
34 Sandelig, siger jeg eder, denne Slægt skal ingenlunde forgå, førend alle disse Ting ere skete.
Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
35 Himmelen og Jorden skulle forgå, men mine Ord skulle ingenlunde forgå.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
36 Men om den Dag og Time ved ingen, end ikke Himmelens Engle, heller ikke Sønnen, men kun Faderen alene.
“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
37 Og ligesom Noas dage vare, således skal Menneskesønnens Tilkommelse være.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
38 Thi ligesom de i Dagene før Syndfloden åde og drak, toge til Ægte og bortgiftede, indtil den Dag, da Noa gik ind i Arken,
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
39 og ikke agtede det, førend Syndfloden kom og tog dem alle bort, således skal også Menneskesønnens Tilkommelse være.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
40 Da skulle to Mænd være på Marken; den ene tages med, og den anden lades tilbage.
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
41 To Kvinder skulle male på Kværnen; den ene tages med, og den anden lades tilbage.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
42 Våger derfor, thi I vide ikke, på hvilken Dag eders Herre kommer.
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
43 Men dette skulle I vide, at dersom Husbonden vidste. i hvilken Nattevagt Tyven vilde komme, da vågede han og tillod ikke, at der skete Indbrud i hans Hus.
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
44 Derfor vorder også I rede; thi Menneskesønnen kommer i den Time, som I ikke mene.
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
45 Hvem er så den tro og forstandige Tjener, som hans Herre har sat over sit Tyende til at give dem deres Mad i rette Tid?
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
46 Salig er den Tjener, hvem hans Herre, når han kommer, finder handlende således.
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
47 Sandelig, siger jeg eder, han skal sætte ham over alt, hvad han ejer.
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
48 Men dersom den onde Tjener siger i sit Hjerte: Min Herre tøver,
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
49 og så begynder at slå sine Medtjenere og spiser og drikker med Drankerne,
Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
50 da skal den Tjeners Herre komme på den Dag, han ikke venter, og i den Time, han ikke ved,
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
51 og hugge ham sønder og give ham hans Lod sammen med Hyklerne; der skal der være Gråd og Tænders Gnidsel.
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.

< Matthæus 24 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water