< Matthæus 2 >

1 Men da Jesus var født i Bethlehem i Judæa, i Kong Herodes's Dage, se, da kom der vise fra Østerland til Jerusalem og sagde:
Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa,
2 "Hvor er den Jødernes Konge, som er født? thi vi have set hans Stjerne i Østen og ere komne for at tilbede ham."
''Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada.''
3 Men da Kong Herodes hørte det, blev han forfærdet, og hele Jerusalem med ham;
Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.
4 og han forsamlede alle Folkets Ypperstepræster og skriftkloge og adspurgte dem, hvor Kristus skulde fødes.
Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, “Ina za a haifi Almasihun?”
5 Og de sagde til ham: "I Bethlehem i Judæa; thi således er der skrevet ved Profeten:
Suka ce masa, ''A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta,
6 Og du, Bethlehem i Judas Land, er ingenlunde den mindste iblandt Judas Fyrster; thi af dig skal der udgå en Fyrste, som skal vogte mit Folk Israel."
'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'''
7 Da kaldte Herodes hemmeligt de vise og fik af dem nøje Besked om Tiden, da Stjernen havde ladet sig til Syne.
Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana.
8 Og han sendte dem til Bethlehem og sagde: "Går hen og forhører eder nøje om Barnet; men når I have fundet det, da forkynder mig det, for at også jeg kan komme og tilbede det."
Ya aike su Baitalami, ya ce, ''Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada.”
9 Men da de havde hørt Kongen, droge de bort; og se, Stjernen, som de havde set i Østen, gik foran dem, indtil den kom og stod oven over, hvor Barnet var.
Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake.
10 Men da de så Stjernen, bleve de såre meget glade.
Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.
11 Og de gik ind i Huset og så Barnet med dets Moder Maria og faldt ned og tilbade det og oplode deres Gemmer og ofrede det Gaver, Guld og Røgelse og Myrra.
Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur.
12 Og da de vare blevne advarede af Gud i en Drøm, at de ikke skulde vende tilbage til Herodes, droge de ad en anden Vej tilbage til deres Land.
Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.
13 Men da de vare dragne bort, se, da viser en Herrens Engel sig i en Drøm for Josef og siger: "Stå op, og tag Barnet og dets Moder med dig og fly til Ægypten og bliv der, indtil jeg siger dig til; thi Herodes vil søge efter Barnet for at dræbe det."
Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, ''Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi.”
14 Og han stod op og tog Barnet og dets Moder med sig om Natten og drog bort til Ægypten.
A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar.
15 Og han var der indtil Herodes's Død, for at det skulde opfyldes, som er talt af Herren ved Profeten, der siger: "Fra Ægypten kaldte jeg min Søn."
Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, ''Daga Masar na kirawo Da na.''
16 Da Herodes nu så, at han var bleven skuffet af de vise, blev han såre vred og sendte Folk hen og lod alle Drengebørn ihjelslå, som vare i Bethlehem og i hele dens Omegn, fra to År og derunder, efter den Tid, som han havde fået Besked om af de vise.
Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.
17 Da blev det opfyldt, som er talt ved Profeten Jeremias, som siger:
A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya,
18 "En Røst blev hørt i Rama, Gråd og megen Jamren; Rakel græd over sine Børn og vilde ikke lade sig trøste, thi de ere ikke mere."
''An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.
19 Men da Herodes var død, se, da viser en Herrens Engel sig i en Drøm for Josef i Ægypten og siger:
Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce,
20 "Stå op, og tag Barnet og dets Moder med dig, og drag til Israels Land; thi de ere døde, som efterstræbte Barnets Liv."
''Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu.''
21 Og han stod op og tog Barnet og dets Moder med sig og kom til Israels Land.
Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.
22 Men da han hørte, at Arkelaus var Konge over Judæa i sin Fader Herodes's Sted, frygtede han for at komme derhen; og han blev advaret af Gud i en Drøm og drog bort til Galilæas Egne.
Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili
23 Og han kom og tog Bolig i en By, som kaldes Nazareth, for at det skulde opfyldes, som er talt ved Profeterne, at han skulde kaldes Nazaræer.
sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.

< Matthæus 2 >