< Matthæus 14 >

1 På den Tid hørte Fjerdingsfyrsten Herodes Rygtet om Jesus.
A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu,
2 Og han sagde til sine Tjenere: "Det er Johannes Døberen; han er oprejst fra de døde, derfor virke Kræfterne i ham."
sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”
3 Thi Herodes havde grebet Johannes og bundet ham og sat ham i Fængsel for sin Broder Filips Hustru, Herodias's Skyld.
To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus,
4 Johannes sagde nemlig til ham: "Det er dig ikke tilladt at have hende."
gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.”
5 Og han vilde gerne slå ham ihjel, men frygtede for Mængden, thi de holdt ham for en Profet.
Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.
6 Men da Herodes's Fødselsdag kom, dansede Herodias's Datter for dem; og hun behagede Herodes.
A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai,
7 Derfor lovede han med en Ed at give hende, hvad som helst hun begærede.
har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa.
8 Og tilskyndet af sin Moder siger hun: "Giv mig Johannes Døberens Hoved hid på et Fad!"
Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.”
9 Og Kongen blev bedrøvet; men for sine Eders og for Gæsternes Skyld befalede han, at det skulde gives hende.
Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa
10 Og han sendte Bud og lod Johannes halshugge i Fængselet.
ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku.
11 Og hans Hoved blev bragt på et Fad og givet Pigen, og hun bragte det til sin Moder.
Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta.
12 Da kom hans Disciple og toge Liget og begravede ham, og de kom og forkyndte Jesus det.
Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.
13 Og da Jesus hørte det, drog han bort derfra i et Skib til et øde Sted afsides; og da Skarerne hørte det, fulgte de ham til Fods fra Byerne.
Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa.
14 Og da han kom i Land, så han en stor Skare, og han ynkedes inderligt over dem og helbredte deres syge.
Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.
15 Men da det blev Aften, kom Disciplene til ham og sagde: "Stedet er øde, og Tiden er allerede forløben; lad Skarerne gå bort, for at de kunne gå hen i Landsbyerne og købe sig Mad."
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”
16 Men Jesus sagde til dem: "De have ikke nødig at gå bort; giver I dem at spise!"
Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”
17 Men de sige til ham: "Vi have ikke her uden fem Brød og to Fisk."
Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”
18 Men han sagde: "Henter mig dem hid!"
Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.”
19 Og han bød Skarerne at sætte sig ned i Græsset og tog de fem Brød og de to Fisk, så op til Himmelen og velsignede; og han brød Brødene og gav Disciplene dem, og Disciplene gave dem til Skarerne.
Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane.
20 Og de spiste alle og bleve mætte; og de opsamlede det, som blev tilovers af Stykkerne, tolv Kurve fulde
Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu.
21 Men de, som spiste, vare omtrent fem Tusinde Mænd, foruden Kvinder og Børn.
Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.
22 Og straks nødte han sine Disciple til at gå om Bord i Skibet og i Forvejen sætte over til hin Side, medens han lod Skarerne gå bort.
Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron.
23 Og da han havde ladet Skarerne gå bort, gik han op på Bjerget afsides for at bede. Og da det blev silde, var han der alene.
Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai,
24 Men Skibet var allerede midt på Søen og led Nød af Bølgerne; thi Vinden var imod.
jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.
25 Men i den fjerde Nattevagt kom han til dem, vandrende på Søen.
Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin.
26 Og da Disciplene så ham vandre på Søen, bleve de forfærdede og sagde: "Det er et Spøgelse;" og de skrege af Frygt.
Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”
27 Men straks talte Jesus til dem og sagde: "Værer frimodige; det er mig, frygter ikke!"
Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
28 Men Peter svarede ham og sagde: "Herre! dersom det er dig, da byd mig at komme til dig på Vandet!"
Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”
29 Men han sagde: "Kom!" Og Peter trådte ned fra Skibet og vandrede på Vandet for at komme til Jesus.
Ya ce, “Zo.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu.
30 Men da han så det stærke Vejr, blev han bange; og da han begyndte at synke, råbte han og sagde: "Herre, frels mig!"
Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
31 Og straks udrakte Jesus Hånden og greb ham, og han siger til ham: "Du lidettroende, hvorfor tvivlede du?"
Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”
32 Og da de stege op i Skibet, lagde Vinden sig.
Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta.
33 Men de, som vare i Skibet, faldt ned for ham og sagde: "Du er sandelig Guds Søn."
Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”
34 Og da de vare farne over, landede de i Genezareth.
Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret.
35 Og da Folkene på det Sted kendte ham, sendte de Bud til hele Egnen der omkring og bragte alle de syge til ham.
Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu
36 Og de bade ham, at de blot måtte røre ved Fligen af hans Klædebon; og alle de, som rørte derved, bleve helbredede.
suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

< Matthæus 14 >