< Markus 14 >

1 Men to Dage derefter var det Påske og de usyrede Brøds Højtid. Og Ypperstepræsterne og de skriftkloge søgte, hvorledes de med List kunde gribe og ihjelslå ham.
To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
2 Thi de sagde: "Ikke på Højtiden, for at der ikke skal blive Oprør iblandt Folket."
Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
3 Og da han var i Bethania, i Simon den spedalskes Hus, kom der, medens han sad til Bords, en Kvinde, som havde en Alabastkrukke med ægte, såre kostbar Nardussalve; og hun sønderbrød Alabastkrukken og udgød den på hans Hoved.
Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
4 Men der var nogle, som bleve vrede hos sig selv og sagde: "Hvortil er denne Spilde af Salven sket?
Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
5 Denne Salve kunde jo være solgt for mere end tre Hundrede Denarer og være given til de fattige." Og de overfusede hende.
Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
6 Men Jesus sagde: "Lader hende være, hvorfor volde I hende Fortrædeligheder? Hun har gjort en god Gerning imod mig.
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
7 De fattige have I jo altid hos eder, og når I ville, kunne I gøre vel imod dem; men mig have I ikke altid.
Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
8 Hun gjorde, hvad hun kunde; hun salvede forud mit Legeme til Begravelsen.
Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
9 Sandelig, siger jeg eder, hvor som helst i hele Verden Evangeliet bliver prædiket, skal også det, som hun har gjort, omtales til hendes Ihukommelse."
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
10 Og Judas Iskariot, en af de tolv, gik hen til Ypperstepræsterne for at forråde ham til dem.
Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
11 Men da de hørte det, bleve de glade, og de lovede at give ham Penge; og han søgte, hvorledes han kunde få Lejlighed til at forråde ham.
Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
12 Og på de usyrede Brøds første Dag, da man slagtede Påskelammet, sige hans Disciple til ham: "Hvor vil du, at vi skulle gå hen og træffe Forberedelse til, at du kan spise Påskelammet?"
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
13 Og han sender to af sine Disciple og siger til dem: "Går ind i Staden, så skal der møde eder en Mand, som bærer en Vandkrukke; følger ham;
Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
14 og hvor han går ind, der skulle I sige til Husbonden: Mesteren siger: Hvor er mit Herberge, hvor jeg kan spise Påskelammet med mine Disciple?
Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
15 Og han skal vise eder en stor Sal, opdækket og rede; og der skulle I berede det for os."
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
16 Og hans Disciple gik bort og kom ind i Staden og fandt det, således som han havde sagt dem; og de beredte Påskelammet.
Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
17 Og da det var blevet Aften, kommer han med de tolv.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
18 Og medens de sade til Bords og spiste, sagde Jesus: "Sandelig, siger jeg eder, en af eder, som spiser med mig, vil forråde mig."
Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
19 De begyndte at bedrøves og at sige til ham, en efter en: "Det er dog vel ikke mig?"
Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
20 Men han sagde til dem: "En af de tolv, den, som dypper med mig i Fadet
Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
21 Thi Menneskesønnen går vel bort, som der er skrevet om ham; men ve det, Menneske ved hvem Menneskesønnen bliver forrådt! Det var godt for det Menneske, om han ikke var født."
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
22 Og medens de spiste, tog han Brød, velsignede og brød det og gav dem det og sagde: "Tager det; dette er mit Legeme."
Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
23 Og han tog en Kalk, takkede og gav dem den; og de drak alle deraf.
Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
24 Og han sagde til dem: "Dette er mit Blod, Pagtens, hvilket udgydes for mange.
Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
25 Sandelig, siger jeg eder, at jeg skal ingen Sinde mere drikke af Vintræets Frugt indtil den Dag, da jeg skal drikke den ny i Guds Rige."
Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
26 Og da de havde sunget Lovsangen, gik de ud til Oliebjerget
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
27 Og Jesus siger til dem: "I skulle alle forarges; thi der er skrevet: Jeg vil slå Hyrden, og Fårene skulle adspredes.
Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
28 Men efter at jeg er bleven oprejst, vil jeg gå forud for eder til Galilæa."
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
29 Men Peter sagde til ham: "Dersom de endog alle forarges, vil jeg dog ikke forarges."
Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
30 Og Jesus siger til ham: "Sandelig siger jeg dig, i Dag, i denne Nat, førend Hanen galer to Gange, skal du fornægte mig tre Gange."
Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
31 Men han sagde end yderligere: "Om jeg end skulde dø med dig, vil jeg ingenlunde fornægte dig." Men ligeså sagde de også alle.
Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
32 Og de komme til en Gård, hvis Navn var Gethsemane; og han siger til sine Disciple "Sætter eder her, imedens jeg beder."
Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
33 Og han tager Peter og Jakob og Johannes med sig, og han begyndte at forfærdes og svarlig at ængstes.
Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
34 Og han siger til dem: "Min Sjæl er dybt bedrøvet indtil Døden; bliver her og våger!"
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
35 Og han gik lidt frem, kastede sig ned på Jorden og bad om, at den Time måtte gå ham forbi, om det var muligt.
Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
36 Og han sagde: "Abba Fader! alting er dig muligt; tag denne Kalk fra mig; dog ikke hvad jeg vil, men hvad du vil."
Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
37 Og han kommer og finder dem sovende og siger til Peter: "Simon, sover du? Kunde du ikke våge een Time?
Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
38 Våger, og beder, for at I ikke skulle falde i Fristelse; Ånden er vel redebon, men Kødet er skrøbeligt."
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
39 Og han gik atter hen og bad og sagde det samme Ord,
Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
40 Og han vendte tilbage og fandt dem atter sovende; thi deres Øjne vare betyngede, og de vidste ikke, hvad de skulde svare ham.
Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
41 Og han kommer tredje Gang og siger til dem: "Sove I fremdeles og hvile eder? Det er nok; Timen er kommen; se, Menneskesønnen forrådes i Synderes Hænder.
Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
42 Står op, lader os gå; se, han, som forråder mig, er nær."
Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
43 Og straks, medens han endnu talte, kommer Judas, en af de tolv, og med ham en stor Skare med Sværd og Knipler fra Ypperstepræsterne og de skriftkloge og de Ældste.
Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
44 Men han, som forrådte ham, havde givet dem et aftalt Tegn og sagt: "Den, som jeg kysser, ham er det; griber ham, og fører ham sikkert bort!"
Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
45 Og da han kom, trådte han straks hen til ham og siger: "Rabbi! Rabbi!" og han kyssede ham.
Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
46 Men de lagde Hånd på ham og grebe ham.
Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
47 Men en af dem, som stode hos, drog Sværdet, slog Ypperstepræstens Tjener og afhuggede hans Øre.
Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
48 Og Jesus svarede og sagde til dem: "I ere gåede ud som imod en Røver, med Sværd og med Knipler for at fange mig.
Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
49 Daglig var jeg hos eder i Helligdommen og lærte, og I grebe mig ikke; men dette sker, for af Skrifterne skulle opfyldes."
Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
50 Og de forlode ham alle og flyede.
Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
51 Og en enkelt, et ungt Menneske, som havde et Linklæde over det blotte Legeme, fulgte med ham; og de gribe ham;
Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
52 men han slap Linklædet og flygtede nøgen.
sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
53 Og de førte Jesus hen til Ypperstepræsten; og alle Ypperstepræsterne og de Ældste og de skriftkloge komme sammen hos ham.
Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
54 Og Peter fulgte ham i Frastand til ind i Ypperstepræstens Gård, og han sad hos Svendene og varmede sig ved Ilden.
Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
55 Men Ypperstepræsterne og hele Rådet søgte Vidnesbyrd imod Jesus, for at de kunde aflive ham; og de fandt intet.
Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
56 Thi mange sagde falsk Vidnesbyrd imod ham, men Vidnesbyrdene stemte ikke overens.
Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
57 Og nogle stode op og vidnede falsk imod ham og sagde:
Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
58 "Vi have hørt ham sige: Jeg vil nedbryde dette Tempel, som er gjort med Hænder, og i tre Dage bygge et andet, som ikke er gjort med Hænder."
“Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
59 Og end ikke således stemte deres Vidnesbyrd overens.
Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
60 Og Ypperstepræsten stod op midt iblandt dem og spurgte Jesus og sagde: "Svarer du slet intet på, hvad disse vidne imod dig?"
Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
61 Men han tav og svarede intet. Atter spurgte Ypperstepræsten ham og siger til ham: "Er du Kristus, den Højlovedes Søn?"
Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
62 Men Jesus sagde: "Jeg er det; og I skulle se Menneskesønnen sidde ved Kraftens højre Hånd og komme med Himmelens Skyer."
Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
63 Men Ypperstepræsten sønderrev sine Klæder og sagde: "Hvad have vi længere Vidner nødig?
Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
64 I have hørt Gudsbespottelsen; hvad tykkes eder?" Men de fældede alle den Dom over ham, at han var skyldig til Døden.
Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
65 Og nogle begyndte af spytte på ham og tilhylle hans Ansigt og give ham Næveslag og sige til ham: "Profeter!" og Svendene modtoge ham med Slag på Kinden.
Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
66 Og medens Peter var nedenfor i Gården, kommer en af Ypperstepræstens Piger,
Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
67 og da hun ser Peter varme sig, ser hun på ham og siger: "Også du var med Nazaræeren, med Jesus."
Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
68 Men han nægtede og sagde: "Jeg hverken ved eller forstår, hvad du siger;" og han gik ud i Forgården, og Hanen galede.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
69 Og Pigen så ham og begyndte atter at sige til dem, som stode hos: "Denne er en af dem."
Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
70 Men han nægtede det atter. Og lidt derefter sagde atter de, som stode hos, til Peter: "Sandelig, du er en af dem; du er jo også en Galilæer."
Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
71 Men han begyndte at forbande sig og sværge: "Jeg kender ikke dette Menneske, om hvem I tale."
Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
72 Og straks galede Hanen anden Gang. Og Peter kom det Ord i Hu, som Jesus sagde til ham: "Førend Hanen galer to Gange, skal du fornægte mig tre Gange." Og han brast i Gråd.
Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.

< Markus 14 >