< Markus 12 >

1 Og han begyndte at tale til dem i Lignelser: "En Mand plantede en Vingård og satte et Gærde derom og gravede en Perse og byggede et Tårn, og han lejede den ud til Vingårdsmænd og drog udenlands.
Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
2 Og da Tiden kom, sendte han en Tjener til Vingårdsmændene, for at han af Vingårdsmændene kunde få af Vingårdens Frugter.
Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
3 Og de grebe ham og sloge ham og sendte ham tomhændet bort.
Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
4 Og han sendte atter en anden Tjener til dem; og ham sloge de i Hovedet og vanærede.
Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
5 Og han sendte en anden; og ham sloge de ihjel; og mange andre; nogle sloge de, og andre dræbte de.
Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
6 Endnu een havde han, en elsket Søn; ham sendte han til sidst til dem, idet han sagde: "De ville undse sig for min Søn."
“Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
7 Men hine Vingårdsmænd sagde til hverandre: "Der er Arvingen; kommer lader os slå ham ihjel, så bliver Arven vor."
“Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
8 Og de grebe ham og sloge ham ihjel og kastede ham ud af Vingården.
Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
9 Hvad vil da Vingårdens Herre gøre? Han vil komme og ødelægge Vingårdsmændene og give Vingården til andre.
“To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
10 Have I ikke også læst dette Skriftord: Den Sten, som Bygningsmændene forkastede, den er bleven til en Hovedhjørnesten?
Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
11 Fra Herren er dette kommet, og det er underligt for vore Øjne."
Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
12 Og de søgte at gribe ham, men de frygtede for Mængden; thi de forstode, at han sagde denne Lignelse imod dem; og de forlode ham og gik bort.
Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
13 Og de sendte nogle til ham af Farisæerne og af Herodianerne, for at de skulde fange ham i Ord.
Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
14 Og de kom og sagde til ham: "Mester! vi vide, at du er sanddru og ikke bryder dig om nogen; thi du ser ikke på Menneskers Person, men lærer Guds Vej i Sandhed. Er det tilladt at give Kejseren Skat eller ej? Skulle vi give eller ikke give?"
Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
15 Men da han så deres Hykleri, sagde han til dem: "Hvorfor friste I mig? Bringer mig en Denar", for at jeg kan se den."
Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
16 Men de bragte den. Og han siger til dem: "Hvis Billede og Overskrift er dette?" Men de sagde til ham: "Kejserens."
Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
17 Og Jesus sagde til dem: "Giver Kejseren, hvad Kejserens er, og Gud, hvad Guds er." Og de undrede sig over ham.
Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
18 Og der kommer Saddukæere til ham, hvilke jo sige, at der ingen Opstandelse er, og de spurgte ham og sagde:
Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
19 "Mester! Moses har foreskrevet os, at når nogens Broder dør og og efterlader, en Hustru og ikke efterlader noget Barn, da skal hans Broder tage hans Hustru og oprejse sin Broder Afkom.
Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
20 Der var syv Brødre; og den første tog en Hustru, og da han døde, efterlod han ikke Afkom.
To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
21 Og den anden tog hende og døde uden at efterlade Afkom, og den tredje ligeså.
Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
22 Og alle syv, de efterlode ikke Afkom. Sidst af dem alle døde og så Hustruen.
A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
23 I Opstandelsen, når de opstå, hvem af dem skal så have hende til Hustru? Thi de have alle syv haft hende til Hustru."
To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
24 Jesus sagde til dem: "Er det ikke derfor, I fare vild, fordi I ikke kende Skrifterne, ej heller Guds Kraft?
Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
25 Thi når de opstå fra de døde, da tage de hverken til Ægte eller bortgiftes, men de ere som Engle i Himlene.
Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
26 Men hvad de døde angår, at de oprejses, have I da ikke læst i Mose Bog i Stedet om Tornebusken, hvorledes Gud talede til ham og sagde: Jeg er Abrahams Gud og Isaks Gud og Jakobs Gud?
Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
27 Han er ikke dødes, men levendes Gud; I fare meget vild."
Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
28 Og en af de skriftkloge, som havde hørt deres Ordskifte og set, at han svarede dem godt, kom til ham og spurgte ham: "Hvilket Bud er det første af alle?"
Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
29 Jesus svarede: "Det første er: Hør Israel! Herren, vor Gud, Herren er een;
Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
30 og du skal elske Herren, din Gud af hele dit Hjerte og af hele din Sjæl og af hele dit Sind og af hele din Styrke.
Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
31 Et andet er dette: Du skal elske din Næste som dig selv. Større end disse er intet andet Bud."
Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
32 Og den skriftkloge sagde til ham: "Rigtigt, Mester, og med Sandhed har du sagt, at han er een, og der er ingen anden foruden ham.
Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
33 Og at elske ham af hele sit Hjerte og af hele sin Forstand og af hele sin Styrke og at elske sin Næste som sig selv, det er mere end alle Brændofrene og Slagtofrene."
Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
34 Og da Jesus så, at han svarede forstandigt, sagde han til ham: "Du er ikke langt fra Guds Rige." Og ingen vovede mere at rette Spørgsmål til ham.
Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
35 Og da Jesus lærte i Helligdommen, tog han til Orde og sagde: "Hvorledes sige de skriftkloge, at Kristus er Davids Søn?
Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
36 David selv sagde ved den Helligånd: Herren sagde til min Herre: Sæt dig ved min, højre Hånd, indtil jeg får lagt dine Fjender som en Skammel for dine Fødder.
Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
37 David selv kalder ham Herre; hvorledes er han da hans Søn?" Og den store Skare hørte ham gerne.
Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
38 Og han sagde i sin Undervisning: "Tager eder i Vare for de skriftkloge, som gerne ville gå i lange Klæder og lade sig hilse på Torvene
Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
39 og gerne ville have de fornemste Pladser i Synagogerne og sidde øverst til Bords ved Måltiderne;
Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
40 de, som opæde Enkers Huse og på Skrømt bede længe, disse skulle få des hårdere Dom."
Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
41 Og han satte sig lige over for Tempelblokken og så, hvorledes Mængden lagde Penge i Blokken, og mange rige lagde meget deri.
Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
42 Og der kom en fattig Enke og lagde to Skærve i, hvilket er en Hvid".
Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
43 Og han kaldte sine Disciple til sig og sagde til dem: "Sandelig, siger jeg eder, denne fattige Enke har lagt mere deri end alle de som lagde i Tempelblokken.
Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
44 Thi de lagde alle af deres Overflod; men hun lagde af sin Fattigdom alt det, hun havde, sin hele Ejendom."
Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”

< Markus 12 >