< Malakias 3 >

1 Se, jeg sender min Engel, og han skal bane Vej for mit Åsyn; og til sit Tempel kommer i et Nu den Herre, I søger, og Pagtens Engel, som I længes efter; se, han kommer, siger Hærskarers HERRE.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 Men hvo kan udholde den Dag, han kommer, og hvo kan stå, når han kommer til Syne? Han er jo som Metalsmelterens Ild og Tvætternes Lud.
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 Han sidder og smelter og renser Sølv; han renser Levis Sønner, lutrer dem som Guld og Sølv, så de kan frembære Offergave for HERREN i Retfærdighed,
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 at Judas og Jerusalems Offergave må være HERREN liflig som i fordums Dage, i henrundne År.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 Jeg nærmer mig eder til Dom og vidner i Hast mod Troldmændene, Ægteskabsbryderne, Menederne og dem, som undertrykker Daglejere, Enker og faderløse, gør fremmede Uret og ikke frygter mig, siger Hærskarers HERRE.
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 Thi jeg, HERREN, er ikke blevet en anden, men I har ikke ophørt at være Jakobsønner".
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Siden eders Fædres Dage er I afveget fra mine Bud og har ikke holdt dem. Vend om til mig, så vil jeg vende om til eder, siger Hærskarers HERRE. Og I spørger: "Hvorledes skal vi vende os?"
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 Skal et Menneske bedrage Gud? I bedrager mig jo! Og I spørger:"Hvorved har vi bedraget dig?" Med Tienden og Offerydelsen!
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 I trues med Forbandelse og bedrager dog mig, ja alt Folket gør det!
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Bring hele Tienden tiI Forrådshuset, så der kan være Mad i mit Hus; sæt mig på Prøve dermed, siger Hærskarers HERRE, om jeg da ikke åbner eder Himmelens Sluser og udøser Velsignelse over eder i Overmål.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Jeg vil for eders Skyld skræmme Æderne, så at de ikke ødelægger eder Landets Afgrøde, og Vinstokken på Marken skal ikke slå eder fejl, siger Hærskarers HERRE.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Og alle Folkene skal love eder, fordi l har et yndigt Land, siger Hærskarers HERRE.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 I taler stærke Ord imod mig, siger HERREN. Og I spørger: "Hvad taler vi imod dig?"
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 I siger: "Det er ørkesløst at tjene Gud; hvad vinder vi ved at opfylde hans Krav og gå sørgeklædte for Hærskarers HERREs Åsyn?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 Nej, vi må love de frække! De øver Gudløshed og kommer til Vejrs; de frister Gud og slipper godt derfra."
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Da talte de, som frygter HERREN, med hverandre. Og HERREN lyttede og hørte efter, og en Bog blev skrevet for hans Åsyn, for at de kunde ihukommes, som frygter HERREN og slår Lid til hans Navn.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 Den Dag jeg griber ind, skal de tilhøre mig som mit Eje, siger Hærskarers HERRE, og jeg vil handle nænsomt med dem, som en Fader handler nænsomt med sin Søn, der tjener ham.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 Da skal l atter kende Forskel på retfærdig og gudløs, på den, som tjener Gud, og den, som ikke tjener ham.
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malakias 3 >