< Lukas 7 >
1 Men da han havde fuldendt alle sine Ord i Folkets Påhør, gik han ind i Kapernaum.
Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
2 Men en Høvedsmands Tjener, som denne holdt meget af, var syg og nær ved at dø.
Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
3 men da han hørte om Jesus, sendte han nogle af Jødernes Ældste til ham og bad ham om, at han vilde komme og helbrede hans Tjener.
Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
4 Men da de kom til Jesus, bade de ham indtrængende og sagde: "Han er vel værd, at du gør dette for ham;
Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
5 thi han elsker vort Folk, og han har bygget Synagogen for os."
saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6 Og Jesus gik med dem. Men da han allerede ikke var langt fra Huset, sendte Høvedsmanden nogle Venner og lod ham sige: "Herre! umag dig ikke; thi jeg er ikke værdig til, at du skal gå ind under mit Tag.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
7 Derfor agtede jeg heller ikke mig selv værdig til at komme til dig; men sig det med et Ord, så bliver min Dreng helbredt.
Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
8 Jeg er jo selv et Menneske, som står under Øvrighed og har Stridsmænd under mig; og siger jeg til den ene: Gå! så går han; og til den anden: Kom! så kommer han; og til min Tjener: Gør dette! så gør han det."
Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
9 Men da Jesus hørte dette, forundrede han sig over ham; og han vendte sig om og sagde til Skaren, som fulgte ham: "Jeg siger eder, end ikke i Israel har jeg fundet så stor en Tro."
Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
10 Og da de, som vare udsendte, kom tilbage til Huset, fandt de den syge Tjener sund.
Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11 Og det skete Dagen derefter, at han gik til en By, som hed Nain, og der gik mange af hans Disciple og en stor Skare med ham.
Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
12 Men da han nærmede sig Byens Port, se, da blev en død båren ud, som var sin Moders enbårne Søn, og hun var Enke; og en stor Skare fra Byen gik med hende.
Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
13 Og da Herren så hende, ynkedes han inderligt over hende og sagde til hende: "Græd ikke!"
Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
14 Og han trådte til og rørte ved Båren; men de, som bare, stode stille, og han sagde: "du unge Mand, jeg siger dig, stå op!"
Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
15 Og den døde rejste sig op og begyndte at tale; og han gav ham til hans Moder.
Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16 Men Frygt betog alle, og de priste Gud og sagde: "Der er en stor Profet oprejst iblandt os, og Gud har besøgt sit Folk."
Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
17 Og denne Tale om ham kom ud i hele Judæa og i hele det omliggende Land.
Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18 Og Johannes's Disciple fortalte ham om alt dette. Og Johannes kaldte to af sine Disciple til sig
Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
19 og sendte dem til Herren og lod sige: "Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?"
Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
20 Og da Mændene kom til ham, sagde de: "Johannes Døberen har sendt os til dig og lader sige: Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?"
Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
21 I den samme Time helbredte han mange for Sygdomme og Plager og onde Ånder og skænkede mange blinde Synet.
A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
22 Og han svarede og sagde til dem: "Går hen, og forkynder Johannes de Ting, som I have set og hørt: Blinde se, lamme gå, spedalske renses, døve høre, døde stå op, Evangeliet forkyndes for fattige;
Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
23 og salig er den, som ikke forarges på mig."
Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
24 Men da Johannes's Sendebud vare gåede bort, begyndte han at sige til Skarerne om Johannes: "Hvad gik I ud i Ørkenen at skue? Et Rør, som bevæges hid og did af Vinden?
Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
25 Eller hvad gik I ud at se? Et Menneske, iført bløde Klæder? Se, de, som leve i prægtige Klæder og i Vellevned, ere i Kongsgårdene.
Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
26 Eller hvad gik I ud at se? En Profet? Ja, siger jeg eder, endog mere end en Profet!
Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27 Han er den, om hvem der er skrevet: Se, jeg sender min Engel for dit Ansigt, han skal berede din Vej foran dig.
Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
28 Jeg siger eder: Iblandt dem, som ere fødte af Kvinder, er ingen større Profet end Johannes; men den mindste i Guds Rige er større end han.
Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29 Og hele Folket, som hørte ham, endog Tolderne, gav Gud Ret, idet de bleve døbte med Johannes's Dåb.
Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
30 Men Farisæerne og de lovkyndige have foragtet Guds Råd med dem selv, idet de ikke bleve døbte af ham.
Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31 Ved hvem skal jeg da ligne denne Slægts Mennesker? og hvem ligne de?
Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
32 De ligne Børn, som sidde på Torvet og råbe til hverandre og sige: Vi blæste på Fløjte for eder, og I dansede ikke, vi sang Klagesange for eder, og I græd ikke.
Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
33 Thi Johannes Døberen kom, som hverken spiste Brød eller drak Vin, og I sige: Han er besat.
Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
34 Menneskesønnen kom, som spiser og drikker, og I sige: Se, en Frådser og en Vindranker, Tolderes og Synderes Ven!
Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
35 Dog Visdommen er retfærdiggjort ved alle sine Børn!"
Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
36 Men en af Farisæerne bad ham om, at han vilde spise med ham; og han gik ind i Farisæerens Hus og satte sig til Bords.
Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
37 Og se, der var en Kvinde, som var en Synderinde i Byen; da hun fik at vide, at han sad til Bords i Farisæerens Hus, kom hun med en Alabastkrukke med Salve;
Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
38 og hun stillede sig bag ved ham, ved hans Fødder og græd og begyndte at væde hans Fødder med sine Tårer og aftørrede dem med sit Hovedhår og kyssede hans Fødder og salvede dem med Salven.
Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39 Men da Farisæeren, som havde indbudt ham, så det, sagde han ved sig selv: "Dersom denne var en Profet, vidste han, hvem og hvordan en Kvinde denne er, som rører ved ham, at hun er en Synderinde."
Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
40 Og Jesus tog til Orde og sagde til ham: "Simon! jeg har noget at sige dig." Men han siger: "Mester, sig frem!"
Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
41 "En Mand, som udlånte Penge, havde to Skyldnere; den ene var fem Hundrede Denarer skyldig. men den anden halvtredsindstyve.
Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
42 Da de ikke havde noget at betale med, eftergav han dem det begge. Hvem af dem vil nu elske ham mest?"
Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
43 Simon svarede og sagde: "Jeg holder for, den, hvem han eftergav mest?" Men han sagde til ham: "Du dømte ret."
Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
44 Og han vendte sig imod Kvinden og sagde til Simon: "Ser du denne Kvinde? Jeg kom ind i dit Hus; du gav mig ikke Vand til mine Fødder; men hun vædede mine Fødder med sine Tårer og aftørrede dem med sit Hår.
Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
45 Du gav mig intet Kys; men hun ophørte ikke med at kysse mine Fødder, fra jeg kom herind.
Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46 Du salvede ikke mit Hoved med Olie; men hun salvede mine Fødder med Salve.
Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
47 Derfor siger jeg dig: Hendes mange Synder ere hende forladte, eftersom hun elskede meget; men den, hvem lidet forlades, elsker lidet."
Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
48 Men han sagde til hende: "Dine Synder ere forladte!"
Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
49 Og de, som sade til Bords med ham, begyndte at sige ved sig selv: "Hvem er denne, som endog forlader Synder?"
Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
50 Men han sagde til Kvinden: "Din Tro har frelst dig, gå bort med Fred!"
Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”