< Lukas 24 >

1 Men på den første Dag i Ugen meget årle kom de til Graven og bragte de vellugtende Urter, som de havde beredt.
Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
2 Og de fandt Stenen bortvæltet fra Graven.
Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
3 Men da de gik derind, fandt de ikke den Herres Jesu Legeme.
Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
4 Og det skete, da de vare tvivlrådige om dette, se, da stode to Mænd for dem i strålende Klædebon.
Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
5 Men da de bleve forfærdede og bøjede deres Ansigter imod Jorden, sagde de til dem: "Hvorfor lede I efter den levende iblandt de døde?
A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
6 Han er ikke her, men han er opstanden; kommer i Hu, hvorledes han talte til eder, medens han endnu var i Galilæa, og sagde,
Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
7 at Menneskesønnen burde overgives i syndige Menneskers Hænder og korsfæstes og opstå på den tredje Dag."
‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
8 Og de kom hans Ord i Hu.
Sai suka tuna da maganarsa.
9 Og de vendte tilbage fra Graven og kundgjorde alle disse Ting for de elleve og for alle de andre.
Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
10 Men det var Maria Magdalene og Johanna og Maria, Jakobs Moder, og de øvrige Kvinder med dem; de sagde Apostlene disse Ting.
Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
11 Og disse Ord kom dem for som løs Tale; og de troede dem ikke.
Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
12 Men Peter stod op og løb til Graven; og da han kiggede derind ser han Linklæderne alene liggende der, og han gik hjem i Undren over det, som var sket.
Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
13 Og se, to af dem vandrede på den samme Dag til en Landsby, som lå tresindstyve Stadier fra Jerusalem, dens Navn var Emmaus.
A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
14 Og de talte med hinanden om alle disse Ting, som vare skete.
Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
15 Og det skete, medens de samtalede og spurgte hinanden indbyrdes, da kom Jesus selv nær og vandrede med dem.
Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
16 Men deres Øjne holdtes til, så de ikke kendte ham.
Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
17 Men han sagde til dem: "Hvad er dette for Ord, som I skifte med hinanden på Vejen?" Og de standsede bedrøvede.
Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
18 Men en af dem, som hed Kleofas, svarede og sagde til ham: "Er du alene fremmed i Jerusalem og ved ikke, hvad der er sket der i disse dage?"
Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
19 Og han sagde til dem: "Hvilket?" Men de sagde til ham: "Det med Jesus af Nazareth, som var en Profet, mægtig i Gerning og Ord for Gud og alt Folket;
Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
20 og hvorledes Ypperstepræsterne og vore Rådsherrer have overgivet ham til Dødsdom og korsfæstet ham.
Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
21 Men vi håbede, at han var den, som skulde forløse Israel. Men med alt dette er det i Dag den tredje Dag, siden dette skete.
Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
22 Men også nogle af vore Kvinder have forfærdet os, idet de kom årle til Graven,
Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
23 og da de ikke fandt hans Legeme, kom de og sagde, at de havde også set et Syn af Engle, der sagde, at han lever.
amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
24 Og nogle af vore gik hen til Graven, og de fandt det således, som Kvinderne havde sagt; men ham så de ikke."
Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
25 Og han sagde til dem: "O I uforstandige og senhjertede til at tro på alt det, som Profeterne have talt!
Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
26 Burde ikke Kristus lide dette og indgå til sin Herlighed?"
Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
27 Og han begyndte fra Moses og fra alle Profeterne og udlagde dem i alle Skrifterne det, som handlede om ham.
Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
28 Og de nærmede sig til Landsbyen, som de gik til; og han lod, som han vilde gå videre.
Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
29 Og de nødte ham meget og sagde: "Bliv hos os; thi det er mod Aften, og Dagen hælder." Og han gik ind for at blive hos dem.
Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
30 Og det skete, da han havde sat sig med dem til Bords, tog han Brødet, velsignede og brød det og gav dem det.
Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
31 Da bleve deres Øjne åbnede, og de kendte ham; og han blev usynlig for dem.
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
32 Og de sagde til hinanden: "Brændte ikke vort Hjerte i os, medens han talte til os på Vejen og oplod os Skrifterne?"
Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
33 Og de stode op i den samme Time og vendte tilbage til Jerusalem og fandt forsamlede de elleve og dem, som vare med dem, hvilke sagde:
Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
34 "Herren er virkelig opstanden og set af Simon."
suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
35 Og de fortalte, hvad der var sket på Vejen, og hvorledes han blev kendt af dem, idet han brød Brødet.
Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
36 Men medens de talte dette, stod han selv midt iblandt dem; og han siger til dem: "Fred være med eder!"
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37 Da forskrækkedes de og betoges af Frygt og mente, at de så en Ånd.
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38 Og han sagde til dem: "Hvorfor ere I forfærdede? og hvorfor opstiger der Tvivl i eders Hjerter?
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39 Ser mine Hænder og mine Fødder, at det er mig selv; føler på mig og ser; thi en Ånd har ikke Kød og Ben, som I se, at jeg har."
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40 Og da han havde sagt dette, viste han dem sine Hænder og sine Fødder.
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41 Men da de af Glæde herover endnu ikke kunde tro og undrede sig, sagde han til dem: "Have I her noget at spise?"
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42 Og de gave ham et Stykke af en stegt Fisk.
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43 Og han tog det og spiste det for deres Øjne.
ya karɓa ya ci a gabansu.
44 Men han sagde til dem: "Dette er mine Ord, som jeg talte til eder, medens jeg endnu var hos eder, at de Ting bør alle sammen opfyldes, som ere skrevne om mig i Mose Lov og Profeterne og Salmerne."
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45 Da oplod han deres Forstand til at forstå Skrifterne.
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
46 Og han sagde til dem: "Således er der skrevet, at Kristus skulde lide og opstå fra de døde på den tredje Dag,
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
47 og at der i hans Navn skal prædikes Omvendelse og Syndernes Forladelse for alle Folkeslagene og begyndes fra Jerusalem.
Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
48 I ere Vidner om disse Ting.
Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
49 Og se, jeg sender min Faders Forjættelse over eder; men I skulle blive i Staden, indtil I blive iførte Kraft fra det høje."
Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
50 Men han førte dem ud til hen imod Bethania, og han opløftede sine Hænder og velsignede dem.
Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
51 Og det skete, idet han velsignede dem, skiltes han fra dem og opløftedes til Himmelen.
Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
52 Og efter at have tilbedt ham vendte de tilbage til Jerusalem med stor Glæde.
Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
53 Og de vare stedse i Helligdommen og priste Gud.
Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.

< Lukas 24 >