< Lukas 21 >
1 Men idet han så op, fik han Øje på de rige, som lagde deres Gaver i Tempelblokken.
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 Men han så en fattig Enke. som lagde to Skærve deri.
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 Og han sagde: "Sandelig, siger jeg eder, at denne fattige Enke lagde mere i end de alle.
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 Thi alle disse lagde af deres Overflod hen til Gaverne; men hun lagde af sin Fattigdom al sin Ejendom, som hun havde."
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 Og da nogle sagde om Helligdommen, at den var prydet med smukke Sten og Tempelgaver. sagde han:
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 "Disse Ting, som I se - der skal komme Dage, da der ikke lades Sten på Sten, som jo skal nedbrydes."
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 Men de spurgte ham og sagde: "Mester! når skal dette da ske? og hvad er Tegnet på, når dette skal ske?"
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 Men han sagde: "Ser til, at I ikke blive forførte; thi mange skulle på mit Navn komme og sige: Det er mig, og: Tiden er kommen nær. Går ikke efter dem!
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 Men når I høre om Krige og Oprør, da forskrækkes ikke; thi dette må først ske, men Enden er der ikke straks."
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Da sagde han til dem: "Folk skal rejse sig imod Folk, og Rige imod Rige.
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 Og store Jordskælv skal der være her og der og Hungersnød og Pest, og der skal ske frygtelige Ting og store Tegn fra Himmelen.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 Men forud for alt dette skulle de lægge Hånd på eder og forfølge eder og overgive eder til Synagoger og Fængsler, og I skulle føres frem for Konger og Landshøvdinger for mit Navns Skyld.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 Det skal falde ud for eder til Vidnesbyrd.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Lægger det da på Hjerte, at I ikke forud skulle overtænke, hvorledes I skulde forsvare eder.
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 Thi jeg, vil give eder Mund og Visdom, som alle eders Modstandere ikke skulle kunne modstå eller modsige.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 Men I skulle endog forrådes af Forældre og Brødre og Frænder og Venner, og de skulle slå nogle af eder ihjel.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 Og I skulle hades af alle for mit Navns Skyld.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 Og ikke et Hår på eders Hoved skal gå tabt.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 Ved eders Udholdenhed skulle I vinde eders Sjæle.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 Men når I se Jerusalem omringet af Krigshære, da forstår, at dens Ødelæggelse er kommen nær.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Da skulle de, som ere i Judæa, fly til Bjergene; og de, som ere inde i Staden, skulle vige bort derfra; og de, som ere på Landet, skulle ikke gå ind i den.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 Thi disse ere Hævnens Dage, da alt, hvad skrevet er, skal opfyldes.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 Men ve de frugtsommelige og dem, som give Die, i de Dage; thi der skal være stor Nød på Jorden og Vrede over dette Folk.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 Og de skulle falde for Sværdets Od og føres fangne til alle Hedningerne; og Jerusalem skal nedtrædes af Hedningerne, indtil Hedningernes Tider fuldkommes.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 Og der skal ske Tegn i Sol og Måne og Stjerner, og på Jorden skulle Folkene ængstes i Fortvivlelse over Havets og Bølgernes Brusen,
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 medens Mennesker forsmægte af Frygt og Forventning om de Ting, som komme over Jorderige; thi Himmelens Kræfter skulle rystes.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 Og da skulle de se Menneskesønnen komme i Sky med Kraft og megen Herlighed.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 Men når disse Ting begynde at ske, da ser op og opløfter eders Hoveder, efterdi eders Forløsning stunder til."
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 Og han sagde dem en Lignelse: "Ser Figentræet og alle Træerne;
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 når de alt springe ud, da se I og skønne af eder selv, at Sommeren nu er nær.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 Således skulle også I, når I se disse Ting ske, skønne, at Guds Rige er nær.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Sandelig, siger jeg eder, at denne Slægt skal ingenlunde forgå, førend det er sket alt sammen.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 Himmelen og Jorden skulle forgå; men mine Ord skulle ingenlunde forgå.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 Men vogter eder, at eders Hjerter ikke, nogen Tid besværes af Svir og Drukkenskab og timelige Bekymringer, så hin dag kommer pludseligt over eder som en Snare.
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 Thi komme skal den over alle dem, der bo på hele Jordens Flade.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Og våger og beder til enhver Tid, for at I må blive i Stand til at undfly alle disse Ting, som skulle ske, og bestå for Menneskesønnen."
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 Men han lærte om Dagene i Helligdommen, men om Nætterne gik han ud og overnattede på det Bjerg, som kaldes Oliebjerget.
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 Og hele Folket kom årle til ham i Helligdommen for at høre ham.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.