< Lukas 15 >

1 Men alle Toldere og Syndere holdt sig nær til ham for at høre ham.
To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa.
2 Og både Farisæerne og de skriftkloge knurrede og sagde: "Denne tager imod Syndere og spiser med dem."
Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”
3 Men han talte denne Lignelse til dem og sagde:
Yesu ya fadi wannan misali, ya ce,
4 "Hvilket Menneske af eder, som har hundrede Får og har mistet eet af dem, forlader ikke de ni og halvfemsindstyve i Ørkenen og går ud efter det, han har mistet, indtil han finder det?
“Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba?
5 Og når han har fundet det, lægger han det på sine Skuldre med Glæde.
Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
6 Og når han kommer hjem, sammenkalder han sine Venner og Naboer og siger til dem: Glæder eder med mig; thi jeg har fundet mit Får, som jeg havde mistet.
In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.'
7 Jeg siger eder: Således skal der være Glæde i Himmelen over een Synder, som omvender sig, mere end over ni og halvfemsindstyve retfærdige, som ikke trænge til Omvendelse.
Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
8 Eller hvilken Kvinde, som har ti Drakmer og taber een Drakme, tænder ikke Lys og fejer Huset og søger med Flid, indtil hun finder den?
Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba?
9 Og når hun har fundet den, sammenkalder hun sine Veninder og Naboersker og siger: Glæder eder med mig; thi jeg har fundet den Drakme, som jeg havde tabt.
In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.'
10 Således, siger jeg eder, bliver der Glæde hos Guds Engle over een Synder, som omvender sig."
Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”
11 Men han sagde: "En Mand havde to Sønner.
Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza,
12 Og den yngste af dem sagde til Faderen: Fader! giv mig den Del af Formuen, som tilfalder mig. Og han skiftede Godset imellem dem.
sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
13 Og ikke mange Dage derefter samlede den yngste Søn alt sit og drog udenlands til et fjernt Land og ødte der sin Formue i et ryggesløst Levned.
Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a.
14 Men da han havde sat alt til, blev der en svær Hungersnød i det samme Land; og han begyndte at lide Mangel.
Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
15 Og han gik hen og holdt sig til en af Borgerne der i Landet, og denne sendte ham ud på sine Marker for at vogte Svin.
Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci.
16 Og han attråede at fylde sin Bug med de Bønner, som Svinene åde; og ingen gav ham noget.
Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
17 Men han gik i sig selv og sagde: Hvor mange Daglejere hos min Fader have ikke Brød i Overflødighed? men jeg omkommer her af Hunger.
Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa!
18 Jeg vil stå op og gå til min Fader og sige til ham: Fader! jeg har syndet imod Himmelen og over for dig,
Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka.
19 jeg er ikke længer værd at kaldes din Søn, gør mig som en af dine Daglejere!
Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'”
20 Og han stod op og kom til sin Fader. Men da han endnu var langt borte, så hans Fader ham og ynkedes inderligt, og han løb til og faldt ham om Halsen og kyssede ham.
Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa.
21 Men Sønnen sagde til ham: Fader! jeg har syndet imod Himmelen og over for dig, jeg er ikke længer værd at kaldes din Søn.
Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
22 Men Faderen sagde til sine Tjenere: Henter det bedste Klædebon frem, og ifører ham det, og giver ham en Ring på hans Hånd og Sko på Fødderne;
Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa.
23 og henter Fedekalven og slagter den, og lader os spise og være lystige!
Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki!
24 Thi denne min Søn var død og er bleven levende igen, han var fortabt og er funden. Og de begyndte at være lystige!
Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
25 Men hans ældste Søn var på Marken, og da han kom og nærmede sig Huset, hørte han Musik og Dans.
A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye.
26 Og han kaldte en af Karlene til sig og spurgte, hvad dette var?
Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa.
27 Men han sagde til ham: Din Broder er kommen, og din Fader har slagtet Fedekalven, fordi han har fået ham sund igen.
Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
28 Men han blev vred og vilde ikke gå ind. Men hans Fader gik ud og bad ham.
Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi.
29 Men han svarede og sagde til Faderen: Se, så mange År har jeg tjent dig, og aldrig har jeg overtrådt noget af dine Bud, og du har aldrig givet mig et Kid, for at jeg kunde være lystig med mine Venner.
Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba,
30 Men da denne din Søn kom, som har fortæret dit Gods med Skøger, slagtede du Fedekalven til ham.
amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
31 Men han sagde til ham: Barn! du er altid hos mig, og alt mit er dit.
Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne.
32 Men man burde være lystig og glæde sig, fordi denne din Broder var død og er bleven levende og var fortabt og er funden."
Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'”

< Lukas 15 >