< Lukas 10 >

1 Men derefter udvalgte Herren også halvfjerdsindstyve andre og sendte dem ud to og to forud for sig, til hver By og hvert Sted, hvorhen han selv vilde komme.
Bayan wadannan abubuwa, Ubangiji ya sake nada wadansu saba'in ya aike su biyu biyu, domin su tafi kowanne birni da wurin da yake niyyan zuwa.
2 Og han sagde til dem: "Høsten er stor, men Arbejderne ere få; beder derfor Høstens Herre om, at han vil sende Arbejdere ud til sin Høst.
Ya ce da su, “Girbin yana da yawa, amma ma'aikatan sun yi kadan. Saboda haka kuyi addu'a sosai ga Ubangijin girbin, domin ya aiko da ma'aikata cikin gonarsa.
3 Går ud! Se, jeg sender eder som Lam midt iblandt Ulve.
Ku tafi, duba na aike ku kamar 'yan raguna cikin kyarkyetai.
4 Bærer ikke Pung, ikke Taske, ej heller Sko; og hilser ingen på Vejen!
Kada ku dauki jakan kudi, ko jakar matafiyi, ko takalma, kada ku gai da kowa a kan hanya.
5 Men hvor I komme ind i et Hus, siger der først: Fred være med dette Hus!
Dukan gidan da ku ka shiga, ku fara cewa, 'Bari salama ta kasance a wannan gida.'
6 Og er der sammesteds et Fredens Barn, skal eders Fred Hvile på ham; men hvis ikke, da skal den vende tilbage til eder igen.
Idan akwai mutum mai salama a gidan, salamar ku za ta kasance a kansa, amma idan babu, salamar ku za ta dawo wurinku.
7 Men bliver i det samme Hus, spiser og drikker, hvad de have; thi Arbejderen er sin Løn værd. I må ikke flytte fra Hus til Hus
Ku zauna a wannan gidan, ku ci ku sha abin da suka tanada maku. Gama ma'aikaci ya wajibci ladansa. Kada ku bi gida gida.
8 Og hvor I komme ind i en By. og de modtage eder, spiser der, hvad der sættes for eder;
Dukan birnin da ku ka shiga kuma sun karbe ku, ku ci abin da suka sa a gabanku.
9 og Helbreder de syge, som ere der, og siger dem: Guds Rige er kommet nær til eder.
Ku warkar da marasa lafiyar da ke wurin. Ku ce da su, 'Mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
10 Men hvor I komme ind i en By og de ikke modtage eder, der skulle I gå ud på dens Gader og sige:
Amma dukan birnin da ku ka shiga, idan ba su karbe ku ba, ku tafi cikin titunansu, ku ce,
11 Endog det Støv, som hænger ved vore Fødder fra eders By, tørre vi af til eder; dog dette skulle I vide, at Guds Rige er kommet nær.
'Ko kurar birninku da ta like a kafafunmu, mun karkabe maku ita a matsayin shaida a kanku! Amma ku sani mulkin Allah ya zo kusa da ku.'
12 Men jeg siger eder, det skal gå Sodoma tåleligere på hin Dag end den By.
Na gaya maku, a ranar shari'a Saduma za ta fi wannan birni samun sauki.
13 Ve dig, Korazin! ve dig, Bethsajda! thi dersom de kraftige Gerninger, som ere skete i eder, vare skete i Tyrus og Sidon, da havde de for længe siden omvendt sig, siddende i Sæk og Aske.
Kaiton ki, Korasinu! Kaiton ki, Baitsaida! Ayyuka masu girma da aka yi a cikinku, da an yi su a cikin Taya da Sidon, da sun tuba tuntuni a zaune cikin toka da tufafin makoki.
14 Men det skal gå Tyrus og Sidon tåleligere ved Dommen end eder.
Amma a ranar shari'a Taya da Sidon za su fi ku samun sauki.
15 Og du, Kapernaum, som er bleven ophøjet indtil Himmelen, du skal nedstødes indtil Dødsriget. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani har zuwa sama za a daukaka ki? Babu, za a gangarar dake har zuwa hadas. (Hadēs g86)
16 Den, som hører eder, hører mig, og den, som foragter eder, foragter mig; men den, som foragter mig, foragter den, som udsendte mig."
Wanda ya saurare ku ya saurare ni, wanda ya ki ku, ya ki ni, kuma wanda ya ki ni, ya ki wanda ya aiko ni.”
17 Men de halvfjerdsindsfyve vendte tilbage med Glæde og sagde: "Herre! også de onde Ånder ere os lydige i dit Navn."
Su saba'in din suka dawo da murna, suna cewa, “Ubangiji, har ma aljanu suna yi mana biyayya, a cikin sunanka.”
18 Men han sagde til dem: "Jeg så Satan falde ned fra Himmelen som et Lyn.
Sai Yesu ya ce masu, “Na ga Shaidan yana fadowa daga sama kamar walkiya.
19 Se, jeg har givet eder Myndighed til at træde på Slanger og Skorpioner og over hele Fjendens Magt, og slet intet skal skade eder.
Duba, na ba ku iko ku taka macizai da kunamai, da kuma kan dukan ikon magabci, kuma ba zai iya yin illa a gareku ba ko kadan.
20 Dog, glæder eder ikke derover, at Ånderne ere eder lydige; men glæder eder over, at eders Navne ere indskrevne i Himlene."
Amma duk da haka kada ku yi murna a kan wannan kadai cewa ruhohi suna yi maku biyayya, amma ku yi murna domin an rubuta sunayenku a cikin sama.”
21 I den samme Stund frydede Jesus sig i den Helligånd og sagde: "Jeg priser dig, Fader, Himmelens og Jordens Herre! fordi du har skjult dette for vise og forstandige og åbenbaret det for umyndige. Ja, Fader! thi således skete det, som var velbehageligt for dig.
Cikin wannan lokacin, ya yi farin ciki kwarai cikin Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Na ba ka girma, ya Uba, Ubangijin sama da kasa. Domin ka rufe wadannan abubuwa daga masu hikima da ganewa, ka bayyana su ga wadanda ba koyayyu ba ne, kamar kananan yara. I, Uba gama haka ne ya gamshe ka.”
22 Alle Ting ere mig overgivne af min Fader; og ingen kender, hvem Sønnen er, uden Faderen, og hvem Faderen er, uden Sønnen og den, for hvem Sønnen vil åbenbare ham."
Dukan abu, Ubana ya damka su gare ni, kuma babu wanda ya san Dan, sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Dan. Sai kuma wanda Dan ya yi niyyar ya bayyana Uban a gareshi.”
23 Og han vendte sig til Disciplene og sagde særligt til dem: "Salige ere de Øjne, som se det, I se.
Ya juya wajen almajiran, ya ce da su a kadaice, “Masu albarka ne su wadanda suka ga abin da kuke gani.
24 Thi jeg siger eder, at mange Profeter og Konger have ville se det, I se, og have ikke set det, og høre det, I høre, og have ikke hørt det."
Na fada maku, annabawa da yawa, da sarakuna da yawa sun so da sun ga abubuwan da kuke gani, amma ba su gani ba. Kuma sun so da sun ji abubuwan da kuke ji, amma ba su ji su ba.”
25 Og se, en lovkyndig stod op og fristede ham og sagde: "Mester! hvad skal jeg gøre, for at jeg kan arve et evigt Liv?" (aiōnios g166)
Sai ga wani malamin shari'ar Yahudawa, ya zo ya gwada shi da cewa, “Malam, me zan yi domin in gaji rai na har abada?” (aiōnios g166)
26 Men han sagde til ham: "Hvad er der skrevet i Loven, hvorledes læser du?".
Sai Yesu ya ce masa, “Yaya kake karanta abin da aka rubuta cikin shari'a?”
27 Men han svarede og sagde til ham: "Du skal elske Herren din Gud af hele dit Hjerte og med hele din Sjæl og med hele din Styrke og med hele dit Sind, og din Næste som dig selv."
Ya amsa ya ce,”Dole ne ka kaunaci Ubangiji Allah da dukan zuciyarka, da dukan ranka da dukan karfinka, da dukan lamirinka. Ka kuma kaunaci makwabcinka kamar kanka.”
28 Men han sagde til ham: "Du svarede ret; gør dette, så skal du leve."
Yesu ya ce ma sa, “Ka amsa daidai, idan ka yi haka za ka rayu.”
29 Men han vilde gøre sig selv retfærdig og sagde til Jesus: "Hvem er da min Næste?"
Amma, malamin ya na so ya 'yantar da kansa, sai ya ce da Yesu, “To, wanene makwabcina?”
30 Men Jesus svarede og sagde: "Et Menneske gik ned fra Jerusalem til Jeriko, og han faldt iblandt Røvere, som både klædte ham af og sloge ham og gik bort og lod ham ligge halvdød.
Ya amsa ya ce, “Wani mutum yana tafiya daga Urushalima za shi Yariko. Sai ya fada hannun mafasa, suka tube shi, suka kwace dukan abin da ya ke da shi, suka yi masa duka, suka bar shi kamar matacce.
31 Men ved en Hændelse gik en Præst den samme Vej ned, og da han så ham, gik han forbi.
Ya zama sai ga wani firist ya na bin wannan hanya, da ya gan shi sai ya bi ta gefe daya ya wuce.
32 Ligeså også en Levit; da han kom til Stedet, gik han hen og så ham og gik forbi.
Haka kuma sai ga wani Balawi, sa'adda ya zo wurin, ya gan shi sai ya bi ta wani gefe ya wuce shi.
33 Men en Samaritan, som var på Rejse, kom til ham, og da han så ham, ynkedes han inderligt.
Amma wani Basamariye, ya na tafiya sa'adda ya zo wurin da mutumin yake, sa'adda ya ga mutumin sai tausayi ya kama shi.
34 Og han gik hen til ham, forbandt hans Sår og gød Olie og Vin deri, løftede ham op på sit eget Dyr og førte ham til et Herberge og plejede ham.
Ya zo inda mutumin yake, ya daure masa raunukan da aka ji masa, yana shafa masu mai da ruwan inabi. Ya dora shi a kan dabbarsa ya kawo shi wurin kwana, ya kula da shi
35 Og den næste Dag tog han to Denarer frem og gav Værten dem og sagde: Plej ham! og hvad mere du lægger ud, vil jeg betale dig, når jeg kommer igen.
Washegari ya kawo dinari biyu, ya ba mai wurin kwanan ya ce 'Ka kula da shi, idan ma ka kashe fiye da haka, idan na dawo zan biya ka.'
36 Hvilken af disse tre tykkes dig nu at have været hans Næste, der var falden iblandt Røverne?"
A cikinsu ukun nan, wanene kake tsammani makwabcin wannan mutum da ya fada hannun 'yan fashi?”
37 Men han sagde: "Han, som øvede. Barmhjertighed imod ham." Og Jesus sagde til ham: "Gå bort, og gør du ligeså!"
Sai malamin ya ce, “Wannan da ya nuna masa jinkai” Sai Yesu yace masa, “Ka je kai ma ka yi haka.”
38 Men det skete, medens de vare på Vandring, gik han ind i en Landsby; og en Kvinde ved Navn Martha modtog ham i sit Hus.
Sa'adda suke tafiya, sai ya shiga cikin wani kauye, sai wata mata mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 Og hun havde en Søster, som hed Maria, og hun satte sig ved Herrens Fødder og hørte på hans Tale.
Tana da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a kafafun Ubangiji tana jin abin da yake fadi.
40 Men Martha havde travlt med megen Opvartning; og hun kom hen og sagde: "Herre! bryder du dig ikke om, at min Søster har ladet mig opvarte ene? Sig hende dog, at hun skal hjælpe mig."
Amma ita Marta ta na ta kokari ta shirya abinci. Sai ta zo wurin Yesu ta ce, “Ubangiji, ba ka damu ba 'yar'uwata ta bar ni ina ta yin aiki ni kadai? Ka ce da ita ta taya ni.”
41 Men Herren svarede og sagde til hende: "Martha! Martha! du gør dig Bekymring og Uro med mange Ting;
Amma Ubangiji ya amsa ya ce da ita, “Marta, Marta, kin damu a kan abubuwa da yawa,
42 men eet er fornødent. Maria har valgt den gode Del, som ikke skal tages fra hende."
amma abu daya ne ya zama dole. Maryamu ta zabi abu mafi kyau, wanda ba za a iya kwace mata ba.”

< Lukas 10 >