< 3 Mosebog 22 >

1 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Sig til Aron og hans Sønner, at de skal behandle Israeliternes Helliggaver, som de helliger mig, med Erefrygt, for at de ikke skal vanhellige mit hellige Navn. Jeg er HERREN!
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
3 Sig til dem: Enhver af alle eders Efterkommere, som i de kommende Slægter i uren Tilstand kommer de Helliggaver nær, Israeliterne helliger HERREN, det Menneske skal udryddes fra mit Åsyn. Jeg er HERREN!
“Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
4 Ingen af Arons Efterkommere, der er spedalsk eller lider af Flåd, må spise noget af Helliggaverne, før han bliver ren; den, der rører ved en, som er uren ved Lig, eller den, fra hvem der går Sæd,
“‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
5 eller den, der rører ved noget Slags Kryb, ved hvilket man bliver uren, eller ved et Menneske, ved hvem man bliver uren, af hvad Art hans Urenhed være kan,
da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
6 enhver, der rører ved noget sådant, skal være uren til Aften og må ikke spise af Helliggaverne, før han har badet sit Legeme i Vand.
duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
7 Når Solen går ned, er han ren, og derefter må han spise af Helliggaverne, thi de er hans Mad.
Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
8 Selvdøde og sønderrevne Dyr må han ikke spise for ikke at gøre sig uren derved. Jeg er HERREN!
Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
9 De skal overholde mine Forskrifter, at de ikke skal pådrage sig Synd og dø derfor, fordi de vanhelliger det. Jeg er HERREN, som helliger dem.
“‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
10 Ingen Lægmand må spise af det hellige; hverken den indvandrede hos Præsten eller hans Daglejer må spise af det hellige.
“‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
11 Men når en Præst for sine Penge køber sig en Træl, da må denne spise deraf, og ligeledes må hans hjemmefødte Trælle spise af hans Mad.
Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
12 Når en Præstedatter ægter en Lægmand, må hun ikke spise af de ydede Helliggaver;
In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
13 men når en Præstedatter bliver Enke eller forstødes uden at have Børn og vender tilbage til sin Faders Hus og er der som i sine unge År, da må hun spise af sin Faders Mad. Men ingen Lægmand må spise deraf.
Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
14 Når nogen af Vanvare kommer til at spise af det hellige, skal han erstatte Præsten det hellige med Tillæg af en Femtedel.
“‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
15 Præsterne må ikke vanhellige de Helliggaver, Israeliterne yder HERREN,
Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
16 og således bringe Brøde og Skyld over dem, når de spiser deres Helliggaver; thi jeg er HERREN, som helliger dem.
ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
17 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Tal til Aron og hans Sønner og alle Israeliterne og sig til dem: Om nogen af Israels Hus eller af de fremmede i Israel bringer sin Offergave, hvad enten det er deres Løfteoffer eller Frivilligoffer, de bringer HERREN som Brændoffer,
“Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
19 så skal I bringe dem således, at I kan vinde Guds Velbehag, et lydefrit Handyr af Hornkvæget, Fårene eller Gederne;
dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
20 I må ikke ofre noget Dyr, der har en Legemsfejl, thi derved vinder I ikke eders Guds Velbehag.
Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
21 Når nogen bringer HERREN et Takoffer af Hornkvæget eller Småkvæget enten for at indfri et Løfte eller som Frivilligoffer, da skal det være et lydefrit Dyr, for at det kan vinde Guds Velbehag; det må ingen som helst Legemsfejl have;
Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
22 et blindt Dyr eller et Dyr med Brud på Lemmerne eller et såret Dyr eller et Dyr, der lider af Bylder, Skab eller Ringorm, sådanne Dyr må I ikke bringe HERREN, og I må ikke lægge noget Ildoffer af den Slags på Alteret for HERREN.
Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
23 Et Stykke Hornkvæg eller Småkvæg med en for lang eller forkrøblet Legemsdel kan du bruge som Frivillig offer, men som Løfteoffer vinder det ikke Guds Velbehag.
Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
24 Dyr med udklemte, knuste, afrevne eller bortskårne Testikler må I ikke bringe HERREN; således må I ikke bære eder ad i eders Land.
Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
25 Heller ikke må I af en Udlænding købe den Slags Dyr og ofre dem som eders Guds Spise, thi de har en Lyde, de har en Legemsfejl; ved dem vinder I ikke Guds Velbehag.
Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
26 HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 Når der fødes et Stykke Hornkvæg, et Får eller en Ged, skal de blive syv Dage hos Moderen; men fra den ottende Dag er de skikkede til at vinde HERRENs Velbehag som Ildoffergave til HERREN.
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28 I må ikke slagte et Stykke Hornkvæg eller Småkvæg samme Dag som dets Afkom.
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29 Når I ofrer et Lovprisningsoffer til HERREN, skal I ofre det således, at det kan vinde eder Guds Velbehag.
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30 Det skal spises samme Dag, I må intet levne deraf til næste Morgen. Jeg er HERREN!
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
31 I skal holde mine Bud og handle efter dem. Jeg er HERREN!
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32 I må ikke vanhellige mit hellige Navn, for at jeg må blive helliget blandt Israeliterne. Jeg er HERREN, som helliger eder,
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33 som førte eder ud af Ægypten for at være eders Gud. Jeg er HERREN!
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”

< 3 Mosebog 22 >