< Klagesangene 5 >

1 HERRE, kom vor skæbne i Hu, sku ned og se vor skændsel!
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Vor Arvelod tilfaldt fremmede, Udlændinge fik vore Huse.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Forældreløse, faderløse er vi, som Enker er vore Mødre.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Vort Drikkevand må vi købe, betale må vi vort Brænde.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Åget trykker vor Nakke, vi trættes og finder ej Hvile.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Ægypten rakte vi Hånd, Assur, for at mættes med Brød.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Vore Fædre, som synded, er borte, og vi må bære deres Skyld.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Over os råder Trælle, ingen frier os fra dem.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Med Livsfare henter vi vort Brød, udsatte for Ørkenens Sværd.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Vor Hud er sværtet som en Ovn af Hungerens svidende Lue.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 De skændede kvinder i Zion, Jomfruer i Judas Byer.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Fyrster greb de og hængte, tog intet Hensyn til gamle.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Ynglinge sattes til Kværnen, under Brændeknippet segnede Drenge.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 De gamle forsvandt fra Porten, de unge fra Strengenes Leg.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Vort Hjertes Glæde er borte, vor Dans er vendt til Sorg.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Kronen faldt af vort Hoved, ve os, at vi har syndet!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Vort Hjerte blev derfor sygt, derfor vort Øje mørkt:
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 For Zions Bjerg, som er øde, Ræve tumler sig der.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Du, HERRE, troner for evigt, fra Slægt til Slægt står din trone.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Hvi glemmer du os bestandig og svigter os alle dage?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Omvend os, HERRE, til dig, så vender vi om, giv os nye Dage, som fordum!
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Eller har du helt stødt os bort, er din Vrede mod os uden Ende?
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Klagesangene 5 >