< Dommer 6 >

1 Men da Israelitterne gjorde, hvad der var ondt i HERRENS Øjne, gav han dem syv År i Midjans Hånd.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
2 Og Midjan fik Overtaget over Israel. For at værge sig mod Midjan indrettede Israelitterne sig de Smuthuller, som findes i Bjergene, Hulerne og Klippeborgene.
Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
3 Hver Gang Israelitterne havde sået, kom Midjaniterne, Amalekiterne og Østens Stammer og drog op imod dem
Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
4 og lejrede sig imod dem, ødelagde Jordens Afgrøde lige til Egnen om Gaza og levnede intet at leve af i Israel, ej heller Småkvæg, Hornkvæg eller Æsler;
Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
5 thi de drog op med deres Hjorde og Telte og kom talrige som Græshopper, så hverken de selv eller deres Kameler kunde tælles, og de trængte ind i Landet for at hærge det.
Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
6 Således blev Israel rent forarmet ved Midjaniternes indfald, og Israelitterne råbte til HERREN.
Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
7 Men da Israelitterne råbte til HERREN over Midjaniterne,
Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
8 sendte han en Profet til dem, og denne sagde til dem: "Så siger HERREN, Israels Gud: Jeg førte eder op fra Ægypten, jeg førte eder ud af Trællehuset,
sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
9 jeg friede eder af Ægyptens Hånd og af deres Hånd, der trængte eder, og jeg drev dem bort foran eder og gav eder deres Land.
Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
10 Og jeg sagde til eder: Jeg er HERREN eders Gud; frygt ikke Amoriternes Guder, i hvis Land I bor! Men I adlød ikke min Røst!"
Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
11 Da kom HERRENs Engel og satte sig under Egen i Ofra, som tilhørte Abiezriten Joasj, medens hans Søn Gideon var ved at tærske Hvede i Vinpersen for at have den i Sikkerhed for Midjaniterne.
Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
12 HERRENs Engel viste sig for ham og sagde til ham: "HERREN er med dig, stærke Kriger!"
Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
13 Men Gideon svarede ham: "Ak, Herre! Hvis HERREN er med os, hvorledes er da alt dette kommet over os? Og hvad er der blevet af alle hans Undergerninger, som vore Fædre fortalte os om, idet de sagde: Førte HERREN os ikke ud af Ægypten? Nu har HERREN forstødt os og givet os i Midjans Hånd!"
Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
14 Da vendte HERREN sig til ham og sagde: "Drag hen i denne din Kraft, så skal du frelse Israel af Midjans Hånd; sandelig, jeg sender dig!"
Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
15 Men han svarede ham: "Ak, Herre! Hvorledes skal jeg kunne frelse Israel? Se, min Slægt er den ringeste i Manasse og jeg den yngste i mit Fædrenehus!"
Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
16 Han svarede ham: "HERREN vil være med dig, og du skal hugge Midjaniterne ned alle som een!"
Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
17 Da sagde han til ham: "Hvis jeg har fundet Nåde for dine Øjne, så lad mig få et Tegn på, at det er dig, som taler med mig;
Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
18 gå ikke herfra, før jeg kommer tilbage til dig og bringer dig min Gave og stiller den frem for dig!" Han svarede: "Jeg skal blive, til du kommer tilbage!"
Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
19 Gideon gik da ind og tillavede et Gedekid og usyrede Brød af en Efa Mel; Kødet lagde han i en Kurv, og Suppen hældte han i en Krukke og bar det ud til ham under Egen. Da han kom hen til ham med det,
Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
20 sagde Guds Engel til ham: "Tag Kødet og det usyrede Brød. Læg det på Klippen der og hæld Suppen ud derover!" Og han gjorde det.
Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
21 Da udrakte HERRENs Engel Spidsen af den Stav, han havde i Hånden, og rørte ved Kødet og Brødet. Og Ild slog op af Klippen og fortærede Kødet og Brødet; og HERRENs Engel forsvandt for hans Blik.
Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
22 Gideon skønnede nu, at det havde været HERRENs Engel; og han sagde: "Ve, Herre, HERRE, jeg har jo set HERRENs Engel Ansigt til Ansigt!"
Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
23 Men HERREN sagde til ham: "Fred være med dig! Frygt ikke, du skal ikke dø!"
Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
24 Da byggede Gideon HERREN et Alter der og kaldte det "HERREN er Fred"; det står endnu den Dag i Dag i Abiezriternes Ofra.
Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
25 Samme Nat sagde HERREN til ham: "Tag ti af dine Trælle og en syvårs Tyr; nedbryd din Faders Ba'alsalter og hug Asjerastøtten om, som står derved;
A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
26 byg så af Stensætningen HERREN din Gud et Alter på Toppen af Klippen her og tag Tyren og brænd den som Brændoffer med Træet af den omhuggede Asjerastøtte!"
Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
27 Gideon tog da ti af sine Trælle og gjorde, som HERREN bød ham; men han gjorde det om Natten, thi af Frygt for sin Familie og sine Bysbørn turde han ikke gøre det om Dagen.
Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
28 Da Byens Folk næste Morgen tidlig så Ba'alsalteret nedbrudt, Asjerastøtten ved Siden af hugget om og Tyren ofret på det nybyggede Alter,
Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
29 sagde de til hverandre: "Hvem mon der har gjort det?" Og da de spurgte sig for og foretog en Undersøgelse, blev der sagt, at det var Gideon, Joasjs Søn.
Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
30 Og Byens Folk sagde til Joasj: "Udlever din Søn, for at han kan lide Døden, thi han har nedbrudt Ba'alsalteret og omhugget Asjerastøtten ved Siden af!"
Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
31 Men Joasj svarede alle dem, der stod omkring ham: "Vil I virkelig stride for Ba'al eller hjælpe ham? Den, der strider for ham, skal dø inden i Morgen! Er han Gud, så lad ham stride for sig selv, siden hans Alter er nedbrudt!"
Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
32 Ved den Lejlighed fik Gideon Navnet Jerubba'al, idet man sagde: "Lad Ba'al stride med ham, siden han har nedbrudt hans Alter!"
Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
33 Alle Midjaniterne, Amalekiterne og Østens Stammer sluttede sig sammen, satte over Jordan og slog Lejr på Jizre'elsletten.
To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
34 Da iklædte HERRENs Ånd sig Gideon, og han stødte i Hornet; og Abiezriterne fylkede sig om ham.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
35 Og da han sendte Bud ud i hele Manasse, fylkede de sig også om ham; og han sendte Bud ud i Aser, Zebulon og Naftali, og de drog op før at møde Fjenderne.
Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
36 Da sagde Gideon til Gud: "Hvis du vil frelse Israel ved min Hånd, som du har lovet,
Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
37 så lægger jeg nu dette Fåreskind på Tærskepladsen, og falder der så Dug alene på Skindet, medens Jorden ellers bliver ved at være tør, da ved jeg, at du vil frelse Israel ved min Hånd, som du har lovet."
to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
38 Og det skete således. Da han næste Morgen vred Skindet, pressede han Dug af det, en hel Skålfuld Vand.
Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
39 Men Gideon sagde til Gud: "Vredes ikke på mig, når jeg endnu denne ene Gang taler til dig, lad mig blot denne Gang endnu prøve med Skindet: Lad Skindet alene være tørt, medens der falder Dug på Jorden rundt om!"
Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
40 Da gjorde Gud således om Natten: Skindet alene var ført, men der faldt Dug på Jorden rundt om.
A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.

< Dommer 6 >