< Dommer 14 >

1 Engang Samson kom ned til Timna, så han en af Filisternes Døtre der.
Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
2 Og da han kom tilbage derfra, fortalte han sin Fader og Moder det og sagde: "Jeg har set en Kvinde i Timna, en af Filisternes Døtre; nu må I hjælpe mig at få hende til Hustru!"
Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
3 Hans Fader og Moder svarede ham: "Findes der da ingen Kvinde blandt dine Landsmænds Døtre eller i hele dit Folk, siden du vil gå hen og tage dig en Hustru hos de uomskårne Filistere?" Men Samson svarede sin Fader: "Nej, hende må du hjælpe mig til, thi det er hende, jeg synes om!"
Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
4 Hans Fader og Moder forstod ikke, at det kom fra HERREN, som søgte en Anledning til Strid over for Filisterne. På den Tid havde Filisterne nemlig Magten over Israel.
(Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
5 Samson tog nu med sin Fader og Moder ned til Timna. Da de nåede Vingårdene uden for Timna, se, da kom en ung Løve brølende imod ham.
Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
6 Så kom HERRENs Ånd over ham, og han sønderrev den med sine bare Næver, som var det et Gedekid; men sin Fader og Moder fortalte han ikke, hvad han havde gjort.
Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
7 Derpå drog han ned og bejlede til Kvinden; thi Samson syntes om hende.
Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
8 Da han efter nogen Tids Forløb vendte tilbage for at ægte hende, gik han hen for at se til Løvens Ådsel, og se, da var der en Bisværm og Honning i Løvens Krop.
Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
9 Han tog da Honningen i sine Hænder og spiste deraf, medens han gik videre; og da han kom til sin Fader og Moder, gav han dem noget deraf, og de spiste; men han sagde dem ikke, at han havde taget Honningen fra Løvens Krop.
wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
10 Så drog Samson ned til Kvinden; og de holdt Gilde, som de unge havde for Skik.
To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
11 Da de så ham, udvalgte de tredive Brudesvende til at ledsage ham.
Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
12 Og Samson sagde til dem: "Jeg vil give eder en Gåde at gætte; hvis I i Løbet af de syv Gildedage kan sige mig Løsningen, vil jeg give eder tredive Linnedkjortler og tredive Sæt klæder;
Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
13 men kan I ikke sige mig den, skal I give mig tredive Linnedkjortler og tredive Sæt klæder!" De svarede: "Sig din Gåde frem og lad os høre den!"
In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
14 Da sagde han til dem: "Fra Æderen kom Æde, fra den stærke Sødme!" Men da de tre Dage var omme, havde de ikke kunnet gætte Gåden,
Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
15 og den fjerde Dag sagde de til Samsons Hustru: "Lok din Mand til at sige os Løsningen, ellers brænder vi dig og din Faders Hus inde! Har I budt os herhen for at tage alting fra os?"
A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
16 Da hang Samsons Hustru over ham med Gråd og sagde: "Du hader mig jo og elsker mig ikke! Du har givet mine Landsmænd en Gåde at gætte, og mig har du ikke sagt Løsningen!" Han svarede hende: "Jeg har ikke sagt min Fader eller Moder den, og så skulde jeg sige dig den!"
Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
17 Men hun hang over ham med Gråd, de syv Dage Gildet varede; og den syvende Dag sagde han hende Løsningen, fordi hun plagede ham. Så sagde hun sine Landsmænd Gådens Løsning;
Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
18 og den syvende Dag, før han gik ind i Kammeret, sagde Byens Mænd til ham: "Hvad er sødere end Honning, og hvad er stærkere end en Løve?" Men han svarede dem: "Havde I ikke pløjet med min Kalv, havde I ikke gættet min Gåde!"
Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
19 Da kom HERRENs Ånd over ham, og han drog ned til Askalon, slog tredive Mænd ihjel der, trak deres Tøj af dem og gav Klæderne til dem, der havde sagt Løsningen på Gåden. Og hans Vrede blussede op, og han drog tilbage til sin Faders Hus.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
20 Men Samsons Hustru blev givet til den Brudesvend, som havde været hans Brudefører.
Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.

< Dommer 14 >