< Josua 20 >

1 Og HERREN talede til Josua og sagde
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 "Tal til Israeliterne og sig: Afgiv de Tilflugtsbyer, jeg talede til eder om ved Moses,
“Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
3 for at en Manddraber, der uforsætligt og af Vanvare slår en ihjel, kan ty til dem, så at de kan være eder Tilflugtssteder mod Blodhævneren.
domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
4 Når han tyr hen til en af disse Byer og stiller sig i Byportens Indgang og forebringer sin Sag for Byens Ældste, skal de optage ham i Byen hos sig og anvise ham et Sted, hvor han kan bo bos dem;
Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
5 og når Blodhævneren forfølger ham, må de ikke udlevere Manddraberen til ham, thi han har slået sin Næste ihjel af Vanvare uden i Forvejen at have båret Nag til ham;
In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
6 han skal blive boende i denne By, indtil han har været stillet for Menighedens Domstol, eller den Mand, som på den Tid er Ypperstepræst, dør; derefter kan Manddraberen vende tilbage til sin By og sit Hjem, den By, han er flygtet fra."
Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
7 Da helligede de Kedesj i Galilæa i Naftalis Bjerge, Sikem i Efrims Bjerge og Kirjat-Arba, det er Hebron, i Judas Bjerge.
Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
8 Og østen for Jordan afgav de Bezer i Ørkenen, på Højsletten, af Rubens Stamme, Ramot i Gilead at Gads Stamme og Golan i Basan af Manasses Stamme.
A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
9 Det var de Byer, som fastsattes for alle Israeliterne og de fremmede, som bor iblandt dem, i det Øjemed at enhver, der uforsætligt slår en ihjel, kan ty derhen og undgå Døden for Blodhævnerens Hånd, før han har været stillet for Menighedens Domstol.
In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.

< Josua 20 >