< Josua 13 >

1 Da Josua var blevet gammel og til Års, sagde HERREN til ham: "Du er blevet gammel og til Års, og der er endnu såre meget tilbage af Landet at indtage.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 Dette er det Land, som er tilbage: Hele Filisternes Landområde og alle Gesjuriterne,
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 Landet fra Sjihor østen for Ægypten indtil Ekrons Landemærke i Nord det regnes til Kana'anæerne de fem Filisterfyrster i Gaza, Asdod, Askalon, Gat og Ekron, desuden Avviterne
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 mod Syd, hele Kana'anæerlandet fra Meara, som tilhører Zidonierne, indtil Afek og til Amoriternes Landemærke,
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 og det Land, som mod Øst grænser til Libanon fra Ba'al Gad ved Hermonbjergets Fod til Egnen hen imod Hamat.
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 Alle Indbyggerne i Bjerglandet fra Libanon til Misrefot Majim, alle Zidonierne, vil jeg drive bort foran Israeliterne. Tildel kun Israel det som Ejendom, således som jeg har pålagt dig.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Udskift derfor dette Land som Ejendom til de halvtiende Stammer." Manasses halve Stamme
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 såvel som Rubeniterne og Gaditerne havde nemlig fået deres Arvelod, som Moses gav dem hinsides Jordan, på Østsiden, således som HERRENs Tjener Moses gav dem,
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 fra Aroer ved Arnonflodens Bred og Byen midt nede i Dalen, hele Højsletten fra Medeba til Dibon,
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 alle de Byer, som havde tilhørt Amoriterkongen Sibon, der herskede i Hesjbon, indtil Ammoniternes Landemærke,
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 fremdeles Gilead og Gesjuriternes og Ma'akatiternes Landemærke, hele Hermonbjerget og hele Basan indtil Salka,
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 hele det Rige, der havde tilhørt Og af Basan, som herskede i Asjtarot og Edrei, den sidste, der var tilbage af Refaiterne; Moses havde overvundet dem alle og drevet dem bort.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Men Israeliterne drev ikke Gesjuriterne og Ma'akatiterne bort, så at Gesjur og Ma'akat bor i blandt Israel den Dag i bag.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Kun Levis Stamme gav han ingen Arvelod; HERREN, Israels Gud, er hans Arvelod, således som han tilsagde ham.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 Moses gav Rubeniternes Stamme Land, Slægt for Slægt,
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 og de fik deres Område fra Aroer ved Arnonflodens Bred og Byen midt nede i Dalen, hele Højsletten indtil
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Hesjbon og alle de Byer, som ligger på Højsletten, Dibon, Bamot Ba'al, Bet Ba'al Meon,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 Jaza, Kedemot, Mefa'at,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 Kirjatajim, Sibma, Zeret Sjahar på Dalbjerget,
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 Bet-Peor ved Pisgas Skrænter. Bet-Jesjimot
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 og alle de andre Byer på Højsletten og hele det Rige, der havde tilhørt Amoriterkongen Sibon, som herskede i Hesjbon, hvem Moses havde overvundet tillige med Midjans Fyrster Evi, Rekem, Zur, Hur og Reba, der var Sihons Lydkonger og boede i Landet;
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 også Sandsigeren Bileam, Beors Søn, havde Israeliterne dræbt med Sværdet sammen med de andre af dem, der blev slået ihjel.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 Rubeniternes Grænse blev Jordan; den var Grænseskel. Det var Rubeniternes Arvelod efter deres Slægter, de nævnte Byer med Landsbyer.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 Og Moses gav Gads Stamme, Gaditerne, Land, Slægt for Slægt,
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 og de fik følgende Landområde: Jazer og alle Byerne i Gilead og Halvdelen af Ammoniternes Land indtil Aroer, som ligger østen for Rabba,
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 og Landet fra Hesjbon til Ramat-Mizpe og Betonim, og fra Mahanajim til Lodebars Landemærke;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 og i Lavningen Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot og Zafon, Resten af Kong Sihon af Hesjbons Rige, med Jordan til Grænse, indtil Enden af Kinnerets Sø, hinsides Jordan, på Østsiden.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 Det var Gaditernes Arvelod efter deres Slægter: de nævnte Byer med Landsbyer.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 Og Moses gav Manasses halve Stamme Land, Slægt for Slægt;
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 og deres Landområde strakte sig fra Mahanajim over hele Basan, hele Kong Og af Basans Rige og alle Jairs Teltbyer, som ligger i Basan, tresindstyve Byer,
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 Halvdelen af Gilead og Asjtarot og Edre'i, Ogs Kongsbyer i Basan; det gav han Manasses Søn Makirs Sønner, Halvdelen af Makirs Sønner, Slægt for Slægt.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 Det er alt, hvad Moses udskiftede på Moabs Sletter hinsides Jordan over for Jeriko, på Østsiden.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 Men Levis Stamme gav Moses ingen Arvelod; HERREN, Israels Gud, er deres Arvelod, således som han tilsagde dem.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Josua 13 >