< Johannes 8 >

1 Men Jesus gik til Oliebjerget.
Yesu ya je Dutsen Zaitun.
2 og årle om Morgenen kom han igen i Helligdommen, og hele Folket kom til ham; og han satte sig og lærte dem.
Da sassafe ya dawo Haikali, dukan mutane kuma suka zo wurin sa; yazauna koya masu.
3 Men de skriftkloge og Farisæerne føre en Kvinde til ham, greben i Hor, og stille hende frem i Midten.
Sai marubuta da Farisawa suka kawo mace wadda aka kama ta tana zina. Su ka sa ta a tsakiya.
4 Og de sige til ham: "Mester! denne Kvinde er greben i Hor på fersk Gerning.
Sai su ka ce da shi, “Malam, wannan mace an kama ta tana cikin yin zina.
5 Men Moses bød os i Loven, at sådanne skulle stenes; hvad siger nu du?"
A cikin shari'a, Musa ya bamu umurni mu jejjefe irin wandannan mutume, kai me ka ce game da ita?”
6 Men dette sagde de for at friste ham, for at de kunde have noget at anklage ham for. Men Jesus bøjede sig ned og skrev med Fingeren på Jorden.
Sun fadi haka ne domin su gwada shi su sami abinda za su zarge shi da shi, amma Yesu ya sunkuya yayi rubutu da yatsansa a kasa.
7 Men da de bleve ved at spørge ham, rettede han sig op og sagde til dem: "Den iblandt eder, som er uden Synd, kaste først Stenen på hende!"
Sa'adda suka cigaba da tambayar sa, ya mike tsaye yace masu, “shi wanda ba shi da zunubi a cikin ku, ya fara jifar ta da dutse.”
8 Og han bøjede sig atter ned og skrev på Jorden.
Ya sake sunkuyawa, ya yi rubutu da yatsansa a kasa.
9 Men da de hørte det, gik de bort, den ene efter den anden, fra de ældste til de yngste, og Jesus blev alene tilbage med Kvinden, som stod der i Midten.
Da suka ji haka, sai suka fita dai-dai da dai-dai, kama daga babbansu. A karshe dai aka bar Yesu shi kadai, tare da matar wadda ta ke a tsakiyar su.
10 Men da Jesus rettede sig op og ingen så uden Kvinden, sagde han til hende: "Kvinde! hvor ere de henne? Var der ingen, som fordømte dig?,"
Yesu ya tashi tsaye ya ce da ita, “mace, ina masu zargin ki? Ba wanda ya kashe ki?
11 Men hun sagde: "Herre! ingen." Da sagde Jesus: "Heller ikke jeg fordømmer dig; gå bort, og synd ikke mere!"
Ta ce, “Ba kowa, Ubangiji” Yesu ya ce, “Ni ma ban kashe ki ba. Ki yi tafiyar ki, daga yanzu kada ki kara yin zunubi.”
12 Jesus talte da atter til dem og sagde: "Jeg er Verdens Lys; den, som følger mig, skal ikke vandre i Mørket, men have Livets Lys."
Yesu ya kara yin magana da mutanen cewa, “Ni ne hasken duniya, shi wanda ya biyo ni, ba zai yi tafiya cikin duhu ba, amma za ya sami hasken rai.
13 Da sagde Farisæerne til ham: "Du vidner om dig selv; dit Vidnesbyrd er ikke sandt."
Farisawa suka ce masa, “Kana bada shaida a kan ka, shaidarka ba gaskiya ba ce.”
14 Jesus svarede og sagde til dem: "Om jeg end vidner om mig selv. er mit Vidnesbyrd sandt; thi jeg ved, hvorfra jeg kom, og hvor jeg går hen; men I vide ikke, hvorfra jeg kommer, og hvor jeg går hen.
Yesu ya amsa ya ce masu, “Ko ma na bada shaida a kai na, shaidata gaskiya ce, na san daga inda na fito da inda zan tafi, amma ku baku san daga inda na fito ba, baku kuma san inda zan tafi ba.
15 I dømme efter Kødet; jeg dømmer ingen.
Kuna shari'a ta son kai, ni ko ban yi wa kowa shari'a ba.
16 Men om jeg også dømmer, er min Dom sand; thi det er ikke mig alene, men mig og Faderen, han, som sendte mig.
Ko ma da na yi shari'a, shari'ata gaskiya ce domin ba ni kadai ba ne, amma ina tare da Uba wanda ya aiko ni.
17 Men også i eders Lov er der skrevet, at to Menneskers Vidnesbyrd er sandt.
I, a cikin dokarku an rubuta cewa shaidar mutum biyu gaskiya ce.
18 Jeg er den, der vidner om mig selv, og Faderen, som sendte mig, vidner om mig."
Ni ne ni ke shaidar kaina, kuma Uba wanda ya aiko ni ya na shaida ta.
19 Derfor sagde de til ham: "Hvor er din Fader?" Jesus svarede: "I kende hverken mig eller min Fader; dersom I kendte mig, kendte I også min Fader."
Su ka ce da shi, “Ina ubanka?” Yesu ya amsa ma su ya ce, “baku san ni ba balle Ubana, in da kun san ni da kun san Uba na kuma. “
20 Disse Ord talte Jesus ved Tempelblokken, da han lærte i Helligdommen; og ingen greb ham, fordi hans Time endnu ikke var kommen.
Ya fadi wadannan kalmomi a kusa da wurin ajiya sa'adda ya ke koyarwa a cikin haikali, kuma ba wanda ya kama shi saboda sa'arsa bata yi ba tukuna.
21 Da sagde han atter til dem: "Jeg går bort, og I skulle lede efter mig, og I skulle dø i eders Synd; hvor jeg går hen, kunne I ikke komme."
Ya kara cewa da su,”Zan tafi, za ku neme ni ba za ku same ni ba, za ku mutu cikin zunubinku. Inda ni ke tafiya, ba za ku iya zuwa ba”.
22 Da sagde Jøderne: "Mon han vil slå sig selv ihjel, siden han siger: Hvor jeg går hen, kunne I ikke komme?"
Yahudawa su ka ce,”Zai kashe kansa ne, da ya ce inda ni ke tafiya ba za ku iya zuwa ba?”
23 Og han sagde til dem: "I ere nedenfra, jeg er ovenfra; I ere af denne Verden, jeg er ikke af denne Verden.
Yesu ya ce masu ku daga kasa kuke, Ni kuwa daga bisa ni ke. Ku na wannan duniya ne, Ni kuwa ba na wannan duniya ba ne.
24 Derfor har jeg sagt eder, at I skulle dø i eders Synder; thi dersom I ikke tro, at det er mig, skulle I dø i eders Synder."
Shiyasa na ce maku za ku mutu cikin zunubanku. In ba kun bada gaskiya NI NE ba, za ku mutu cikin zunubanku.
25 De sagde da til ham: "Hvem er du?" Og Jesus sagde til dem: "Just det, som jeg siger eder.
Sai kuma suka ce da shi,”Wanene kai?” Yesu ya ce masu, “Abin da na gaya maku tun daga farko.
26 Jeg har meget at tale og dømme om eder; men den, som sendte mig, er sanddru, og hvad jeg har hørt af ham, det taler jeg til Verden."
Ina da a bubuwa da yawa da zan gaya maku, in kuma hukunta ku a kai. Duk da haka, wanda ya aiko ni, mai gaskiya ne, abubuwan da naji daga wurin sa, wadannan abubuwan su ni ke gaya wa duniya.”
27 De forstode ikke, at han talte til dem om Faderen.
Ba su gane ba yana yi masu magana a kan Uban.
28 Da sagde Jesus til dem: "Når I få ophøjet Menneskesønnen, da skulle I kende, at det er mig, og at jeg gør intet af mig selv; men som min Fader har lært mig, således taler jeg.
Yesu ya ce, “Sa'adda kuka tada Dan Mutum sama sa'annan za ku gane NI NE, kuma ban yi komi domin kaina ba. Kamar yadda Uba ya koya mani, haka nike fadin wadannan abubuwa.
29 Og han, som sendte mig, er med mig; han har ikke ladet mig alene, fordi jeg; gør altid det, som er ham til Behag."
Shi wanda ya aiko ni, yana tare da ni kuma bai bar ni ni kadai ba, domin kullum ina yin abubuwan da suke faranta masa rai.”
30 Da han talte dette, troede mange på ham.
Sa'adda Yesu ya ke fadin wadannan abubuwa, dayawa suka bada gaskiya gare shi.
31 Jesus sagde da til de Jøder, som vare komne til Tro på ham: "Dersom I blive i mit Ord, ere I sandelig mine Disciple,
Yesu ya gayawa wadancan Yahudawa da suka bada gaskiya gare shi, “Idan kun tsaya a cikin magana ta ku almajiraina ne na gaskiya,
32 og I skulle erkende Sandheden, og Sandheden skal frigøre eder."
Kuma za ku san gaskiya, gaskiya kuwa zata 'yantar da ku.”
33 De svarede ham: "Vi ere Abrahams Sæd og have aldrig været nogens Trælle; hvorledes siger du da: I skulle vorde frie?"
Suka amsa masa, “Mu zuriyar Ibrahim ne kuma bamu taba yin bauta wurin kowa ba, yaya za ka ce, 'Za a 'yantar da ku'?”
34 Jesus svarede dem: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, hver den, som gør Synden, er Syndens Træl.
Yesu ya ce masu, “Hakika, hakika, ina ce maku, dukan wanda ya ke aika zunubi bawan zunubi ne.
35 Men Trællen bliver ikke i Huset til evig Tid, Sønnen bliver der til evig Tid. (aiōn g165)
Bawa kuwa, ba ya zama a gida dindindin, da yana zama dindindin. (aiōn g165)
36 Dersom da Sønnen får frigjort eder, skulle I være virkelig frie.
Saboda haka, idan Dan ya 'yantar da ku zaku zama 'yantattu sosai.
37 Jeg ved, at I ere Abrahams Sæd; men I søge at slå mig ihjel, fordi min Tale ikke finder Rum hos eder.
Na san ku zuriyar Ibrahim ne, kuna so ku kashe ni saboda kalma ta bata da wurin zama a cikin ku.
38 Jeg taler det, som jeg har set hos min Fader; så gøre også I det, som I have hørt af eders Fader."
Na fadi abubuwan da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abubuwan da kuka ji daga wurin ubanku.”
39 De svarede og sagde til ham: "Vor Fader er Abraham." Jesus sagde til dem: "Dersom I vare Abrahams Børn, gjorde I Abrahams Gerninger.
Suka amsa suka ce masa, “Ibrahim ne ubanmu” Yesu ya ce masu, “Da ku 'yayan Ibrahim ne da kun yi ayukan da Ibrahim ya yi.
40 Men nu søge I at slå mig ihjel, et Menneske, der har sagt eder Sandheden, som jeg har hørt af Gud; dette gjorde Abraham ikke.
Amma, yanzu kuna so ku kashe ni, mutumin da ya gaya maku gaskiyar da ya ji daga wurin Allah. Ibrahim bai yi haka ba.
41 I gøre eders Faders Gerninger." De sagde til ham: "Vi ere ikke avlede i Hor; vi have een Fader, Gud."
Kuna yin ayyukan ubanku. Suka ce masa, “mu ba a haife mu cikin fasikanci ba, muna da Uba daya: Allah.”
42 Jesus sagde til dem: "Dersom Gud var eders Fader, da elskede I mig; thi jeg er udgået og kommen fra Gud; thi jeg er heller ikke kommen af mig selv, men han har udsendt mig.
Yesu ya ce masu, “Inda Allah Ubanku ne, da kun kaunace ni, gama na zo daga wurin Allah kuma ga ni anan, gama ba domin kaina nazo ba, shine ya aiko ni.
43 Hvorfor forstå I ikke min Tale? fordi I ikke kunne høre mit Ord.
Meyasa baku gane magana ta ba? Ai saboda ba za ku iya jin maganata ba ne.
44 I ere af den Fader Djævelen, og eders Faders Begæringer ville I gøre. Han var en Manddraber fra Begyndelsen af, og han står ikke i Sandheden; thi Sandhed er ikke i ham. Når han taler Løgn, taler han af sit eget; thi han er en Løgner og Løgnens Fader.
Ku na ubanku, shaidan ne, kuma kuna so ku yi nufe-nufe na ubanku. Shi mai kisan kai ne tun daga farko kuma ba ya tsayawa gaskiya saboda da babu gaskiya a cikin sa. Sa'anda yake fadin karya, yana maganar halinsa ne domin shi dama makaryaci ne da uban karya kuma.
45 Men mig tro I ikke, fordi jeg siger Sandheden.
Dayake ina fadin gaskiya baku bada gaskiya gare ni ba.
46 Hvem af eder kan overbevise mig om nogen Synd? Siger jeg Sandhed, hvorfor tro I mig da ikke?
Wanene a cikin ku ya kama ni da zunubi? Idan na fadi gaskiya don me ba ku gaskanta ni ba?
47 Den, som er af Gud, hører Guds Ord; derfor høre I ikke, fordi I ere ikke af Gud."
Shi wanda yake na Allah ya kan ji maganar Allah, ku ba kwa jin maganar Allah da yake ku ba na Allah bane,”
48 Jøderne svarede og sagde til ham: "Sige vi ikke med Rette, at du er en Samaritan og er besat?"
Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Bamu fadi gaskiya ba da muka ce kai Basamariye ne kuma kana da aljan?”
49 Jesus svarede: "Jeg er ikke besat, men jeg ærer min Fader, og I vanære mig.
Yesu ya amsa, “Ni ba ni da aljan, ina girmama Ubana, ku kuma ba kwa girmama ni.”
50 Men jeg søger ikke min Ære; der er den, som søger den og dømmer.
Ba na neman daraja domin kaina, akwai wanda ke nema yana kuma hukuntawa.
51 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, dersom nogen holder mit Ord, skal han i al Evighed ikke se Døden." (aiōn g165)
Hakika, hakika, iIna ce maku, dukan wanda ya kiyaye maganata, ba za ya ga mutuwa ba.” (aiōn g165)
52 Jøderne sagde til ham: "Nu vide vi, at du et besat; Abraham døde og Profeterne, og du siger: Dersom nogen holder mit Ord, han skal i al Evighed ikke smage Døden. (aiōn g165)
Sai Yahudawa su ka ce masa, Yanzu mun sani kana da aljan. Ibrahim da annabawa sun mutu, amma kai ka ce, 'dukan wanda ya yi biyayya da maganata ba zai dandana mutuwa ba'. (aiōn g165)
53 Mon du er større end vor Fader Abraham, som jo døde? også Profeterne døde; hvem gør du dig selv til?"
Ai baka fi ubanmu Ibrahim girma ba wanda ya mutu, ko ka fi shi? Annabawa kuma sun mutu. Wa kake daukar kanka ne?”
54 Jesus svarede: "Dersom jeg ærer mig selv, er min Ære intet; det er min Fader, som ærer mig, han, om hvem I sige, at han er eders Gud.
Yesu ya amsa, “Idan na daukaka kaina, daukaka ta banza ce, Ubana ne ya daukaka ni. Wanda kuka ce shi ne Allahnku.
55 Og I have ikke kendt ham, men jeg kender ham. Og dersom jeg siger: "Jeg kender ham ikke," da bliver jeg en Løgner ligesom I; men jeg kender ham og holder hans Ord.
Ku kuwa ba ku san shi ba, amma ni na san shi. Idan na ce ban san shi ba, na zama kamar ku kenan, makaryaci. Sai dai, Ni na san shi ina kiyaye maganarsa.
56 Abraham, eders Fader, frydede sig til at se min Dag, og han så den og glædede sig."
Ubanku Ibrahim ya yi farinciki da ganin rana ta; ya gan ta kuma ya yi murna.”
57 Da sagde Jøderne til ham: "Du er endnu ikke halvtredsindstyve År gammel, og du har set Abraham?"
Yahudawa su ka ce masa, “Baka kai shekara hamsin ba tukuna, ka taba ganin Ibrahim?”
58 Jesus sagde til dem: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, førend Abraham blev til, har jeg været."
Yesu ya ce masu, “Hakika, hakika, ina ce maku, kafin a haifi Ibrahim, NI NE.”
59 Så toge de Sten for at kaste på ham; men Jesus skjulte sig og gik ud af Helligdommen.
Suka dauki duwatsu za su jefe shi, amma Yesu ya boye kansa, ya fita daga haikali.

< Johannes 8 >