< Johannes 6 >

1 Derefter drog Jesus over til hin Side af Galilæas Sø, Tiberias Søen.
Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
2 Og en stor Skare fulgte ham, fordi de så de Tegn, som han gjorde på de syge.
Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
3 Men Jesus gik op på Bjerget og satte sig der med sine Disciple.
Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
4 Men Påsken, Jødernes Højtid, var nær.
(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5 Da Jesus nu opløftede sine Øjne og så, at en stor Skare kom til ham, sagde han til Filip: "Hvor skulle vi købe Brød, for at disse kunne få noget at spise?"
Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6 Men dette sagde han for at prøve ham; thi han vidste selv, hvad han vilde gøre.
( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7 Filip svarede ham: "Brød for to Hundrede Denarer er ikke nok for dem, til at hver kan få noget lidet."
Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
8 En af hans Disciple, Andreas, Simon Peters Broder, siger til ham:
Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
9 "Her er en lille Dreng, som har fem Bygbrød og to Småfisk; men hvad er dette til så mange?"
“Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
10 Jesus sagde: "Lader Folkene sætte sig ned;" og der var meget Græs på Stedet. Da satte Mændene sig ned, omtrent fem Tusinde i Tallet.
Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Så tog Jesus Brødene og takkede og uddelte dem til dem, som havde sat sig ned; ligeledes også af Småfiskene så meget, de vilde.
Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
12 Men da de vare blevne mætte, siger han til sine Disciple: "Samler de tiloversblevne Stykker sammen, for at intet skal gå til Spilde."
Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
13 Da samlede de og fyldte tolv Kurve med Stykker, som bleve tilovers af de fem Bygbrød fra dem, som havde fået Mad.
Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
14 Da nu Folkene så det Tegn, som han havde gjort, sagde de: "Denne er i Sandhed Profeten, som kommer til Verden."
Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
15 Da Jesus nu skønnede, at de vilde komme og tage ham med Magt for at gøre ham til Konge, gik han atter op på Bjerget, ganske alene.
“Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16 Men da det var blevet Aften, gik hans Disciple ned til Søen.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17 Og de gik om Bord i et Skib og vilde sætte over til hin Side af Søen til Kapernaum. Og det var allerede blevet mørkt, og Jesus var endnu ikke kommen til dem.
Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
18 Og Søen rejste sig, da der blæste en stærk Vind.
Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19 Da de nu havde roet omtrent fem og tyve eller tredive Stadier, se de Jesus vandre på Søen og komme nær til Skibet, og de forfærdedes.
Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
20 Men han siger til dem: "Det er mig; frygter ikke!"
Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
21 Da vilde de tage ham op i Skibet; og straks kom Skibet til Landet, som de sejlede til.
Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22 Den næste dag så Skaren, som stod på hin Side af Søen, at der ikke havde været mere end eet Skib der, og at Jesus ikke var gået om Bord med sine Disciple, men at hans Disciple vare dragne bort alene,
Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
23 (men der var kommet Skibe fra Tiberias nær til det Sted, hvor de spiste Brødet, efter at Herren havde gjort Taksigelse):
Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24 da Skaren nu så, at Jesus ikke var der, ej heller hans Disciple, gik de om Bord i Skibene og kom til Kapernaum for at søge efter Jesus.
Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Og da de fandt ham på hin Side af Søen, sagde de til ham: "Rabbi! når er du kommen hid?"
Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
26 Jesus svarede dem og sagde: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, I søge mig, ikke fordi I så Tegn, men fordi I spiste af Brødene og bleve mætte.
Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
27 Arbejder ikke for den Mad, som er forgængelig, men for den Mad, som varer til et evigt Liv, hvilken Menneskesønnen vil give eder; thi ham har Faderen, Gud selv, beseglet." (aiōnios g166)
Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios g166)
28 Da sagde de til ham: "Hvad skulle vi gøre, for at vi kunne arbejde på Guds Gerninger?"
Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
29 Jesus svarede og sagde til dem: "Dette er Guds Gerning, at I tro på den, som han udsendte."
Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 Da sagde de til ham: "Hvad gør du da for et Tegn, for at vi kunne se det og tro dig? Hvad Arbejde gør du?
Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Vore Fædre åde Manna i Ørkenen, som der er skrevet: Han gav dem Brød fra Himmelen at æde."
Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Da sagde Jesus til dem: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, ikke Moses har givet eder Brødet fra Himmelen, men min Fader giver eder det sande Brød fra Himmelen.
Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 Thi Guds Brød er det, som kommer ned fra Himmelen og giver Verden Liv."
Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Da sagde de til ham: "Herre! giv os altid dette Brød!"
Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 Jesus sagde til dem: "Jeg er Livets Brød. Den, som kommer til mig, skal ikke hungre; og den, som tror på mig, skal aldrig tørste.
Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
36 Men jeg har sagt eder, at I have set mig og dog ikke tro.
Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
37 Alt, hvad Faderen giver mig, skal komme til mig; og den, som kommer til mig, vil jeg ingenlunde kaste ud.
Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38 Thi jeg er kommen ned fra Himmelen, ikke for at gøre min Villie, men hans Villie, som sendte mig.
Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
39 Men dette er hans Villie, som sendte mig, at jeg skal intet miste af alt det, som han har givet mig, men jeg skal oprejse det på den yderste Dag.
Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
40 Thi dette er min Faders Villie, at hver den, som ser Sønnen og tror på ham, skal have et evigt Liv, og jeg skal oprejse ham på den yderste Dag." (aiōnios g166)
Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
41 Da knurrede Jøderne over ham, fordi han sagde: "Jeg er det Brød, som kom ned fra Himmelen,"
Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
42 og de sagde: "Er dette ikke Jesus, Josefs Søn, hvis Fader og Moder vi kende? Hvorledes kan han da sige: Jeg er kommen ned fra Himmelen?"
Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43 Jesus svarede og sagde til dem: "Knurrer ikke indbyrdes!
Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
44 Ingen kan komme til mig, uden Faderen, som sendte mig, drager ham; og jeg skal oprejse ham på den yderste Dag.
Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
45 Der er skrevet hos Profeterne: "Og de skulle alle være oplærte af Gud." Hver den, som har hørt af Faderen og lært, kommer til mig.
A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46 Ikke at nogen har set Faderen, kun den, som er fra Gud, han har set Faderen.
Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
47 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, den, som tror på mig, har et evigt Liv. (aiōnios g166)
Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios g166)
48 Jeg er Livets Brød.
Ni ne Gurasa ta rai.
49 Eders Fædre åde Manna i Ørkenen og døde.
Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 Dette er det Brød, som kommer ned fra Himmelen, at man skal æde af det og ikke dø.
Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 Jeg er det levende Brød, som kom ned fra Himmelen; om nogen æder af dette Brød, han skal leve til evig Tid; og det Brød, som jeg vil give, er mit Kød, hvilket jeg vil give for Verdens Liv." (aiōn g165)
Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn g165)
52 Da kivedes Jøderne indbyrdes og sagde: "Hvorledes kan han give os sit Kød at æde?"
Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
53 Jesus sagde da til dem: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, dersom I ikke æde Menneskesønnens Kød og drikke hans Blod, have I ikke Liv i eder.
Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54 Den, som æder mit Kød og drikker mit Blod, har et evigt Liv, og jeg skal oprejse ham på den yderste Dag. (aiōnios g166)
Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
55 Thi mit Kød er sand Mad, og mit Blod er sand Drikke.
Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Den, som æder mit Kød og drikker mit Blod, han bliver i mig, og jeg i ham.
Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57 Ligesom den levende Fader udsendte mig, og jeg lever i Kraft af Faderen, ligeså skal også den, som æder mig, leve i Kraft af mig.
Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
58 dette er det Brød, som er kommet ned fra Himmelen; ikke som eders Fædre åde og døde. Den, som æder dette Brød, skal leve evindelig." (aiōn g165)
Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 Dette sagde han, da han lærte i en Synagoge i Kapernaum.
Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60 Da sagde mange af hans Disciple, som havde hørt ham: "Dette er en hård Tale; hvem kan høre den?"
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
61 Men da Jesus vidste hos sig selv, at hans Disciple knurrede derover, sagde han til dem: "Forarger dette eder?
Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
62 Hvad om I da få at se, at Menneskesønnen farer op, hvor han var før?
Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
63 Det er Ånden, som levendegør, Kødet gavner intet; de Ord, som jeg har talt til eder, ere Ånd og ere Liv.
Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64 Men der er nogle af eder, som ikke tro." Thi Jesus vidste fra Begyndelsen, hvem det var, der ikke troede, og hvem den var, der skulde forråde ham.
Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Og han sagde: "Derfor har jeg sagt eder, at ingen kan komme til mig, uden det er givet ham af Faderen."
Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
66 Fra den Tid trådte mange af hans Disciple tilbage og vandrede ikke mere med ham.
Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
67 Jesus sagde da til de tolv: "Mon også I ville gå bort?"
Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
68 Simon Peter svarede ham: "Herre! til hvem skulle vi gå hen? Du har det evige Livs Ord; (aiōnios g166)
Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios g166)
69 og vi have troet og erkendt, at du er Guds Hellige."
Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
70 Jesus svarede dem: "Har jeg ikke udvalgt mig eder tolv, og en af eder er en Djævel?"
Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
71 Men han talte om Judas, Simon Iskariots Søn; thi det var ham, som siden skulde forråde ham, skønt han var en af de tolv.
Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.

< Johannes 6 >