< Johannes 2 >

1 Og på den tredje Dag var der et Bryllup i Kana i Galilæa; og Jesu Moder var der.
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 Men også Jesus og hans Disciple bleve budne til Brylluppet.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 Og da Vinen slap op, siger Jesu Moder til ham: "De have ikke Vin."
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus siger til hende: "Kvinde! hvad vil du mig? min Time er endnu ikke kommen."
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 Hans Moder siger til Tjenerne: "Hvad som han siger eder, det skulle I gøre."
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 Men der var der efter Jødernes Renselsesskik fremsat seks Vandkar af Sten, som rummede hvert to eller tre Spande.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus siger til dem: "Fylder Vandkarrene med Vand; " og de fyldte dem indtil det øverste.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 Og han siger til dem: "Øser nu og bærer til Køgemesteren; " og de bare det til ham.
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 Men da Køgemesteren smagte Vandet, som var blevet Vin, og ikke vidste, hvorfra det kom (men Tjenerne, som havde øst Vandet, vidste det), kalder Køgemesteren på Brudgommen og siger til ham:
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 "Hvert Menneske sætter først den gode Vin frem, og når de ere blevne drukne, da den ringere; du har gemt den gode Vin indtil nu."
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 Denne Begyndelse på sine Tegn gjorde Jesus i Kana i Galilæa, og han åbenbarede sin Herlighed; og hans Disciple troede på ham.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 Derefter drog han ned til Kapernaum, han og hans Moder og hans Brødre og hans Disciple, og de bleve der ikke mange Dage.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 Og Jødernes Påske var nær, og Jesus drog op til Jerusalem.
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 Og han fandt siddende i Helligdommen dem, som solgte Okser og Får og Duer, og Vekselerne.
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 Og han gjorde en Svøbe af Reb og drev dem alle ud af Helligdommen, både Fårene og Okserne, og han spredte Vekselerernes Småpenge og væltede Bordene.
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 Og han sagde til dem, som solgte duer: "Tager dette bort herfra; gører ikke min Faders Hus til en Købmandsbod!"
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 Hans Disciple kom i Hu, at der er skrevet: "Nidkærheden for dit Hus vil fortære mig."
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 Da svarede Jøderne og sagde til ham: "Hvad viser du os for et Tegn, efterdi du gør dette?"
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus svarede og sagde til dem: "Nedbryder dette Tempel, og i tre Dage vil jeg oprejse det."
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 Da sagde Jøderne: "I seks og fyrretyve År er der bygget på dette Tempel, og du vil oprejse det i tre Dage?"
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 Men han talte om sit Legemes Tempel.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 Da han så var oprejst fra de døde, kom hans Disciple i Hu, at han havde sagt dette; og de troede Skriften og det Ord, som Jesus havde sagt.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 Men da han var i Jerusalem i Påsken på Højtiden, troede mange på hans Navn, da de så hans Tegn, som han gjorde.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 Men Jesus selv betroede sig ikke til dem, fordi han kendte alle,
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 og fordi han ikke havde nødig, at nogen skulde vidne om Mennesket; thi han vidste selv, hvad der var i Mennesket.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< Johannes 2 >