< Johannes 15 >

1 "Jeg er det sande Vintræ, og min Fader er Vingårdsmanden.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Hver Gren på mig, som ikke bærer Frugt, den borttager han, og hver den, som bærer Frugt, renser han, for at den skal bære mere Frugt.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 I ere allerede rene på Grund af det Ord, som jeg har talt til eder.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Bliver i mig, da bliver også jeg i eder. Ligesom Grenen ikke kan bære Frugt af sig selv, uden den bliver på Vintræet, således kunne I ikke heller, uden I blive i mig.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 Jeg er Vintræet, I ere Grenene. Den, som bliver i mig, og jeg i ham, han bærer megen Frugt; thi uden mig kunne I slet intet gøre.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 Om nogen ikke bliver i mig, han bliver udkastet som en Gren og visner; man sanker dem og kaster dem i Ilden, og de brændes.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 Dersom I blive i mig, og mine Ord blive i eder, da beder, om hvad som helst I ville, og det skal blive eder til Del.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 Derved er min Fader herliggjort, at I bære megen Frugt, og I skulle blive mine Disciple.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 Ligesom Faderen har elsket mig, så har også jeg elsket eder; bliver i min Kærlighed!
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 Dersom I holde mine Befalinger, skulle I blive i min Kærlighed, ligesom jeg har holdt min Faders Befalinger og bliver i hans Kærlighed.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 Dette har jeg talt til eder, for at min Glæde kan være i eder, og eders Glæde kan blive fuldkommen.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 Dette er min Befaling, at I skulle elske hverandre, ligesom jeg har elsket eder.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 Større Kærlighed har ingen end denne, at han sætter sit Liv til for sine Venner.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 I ere mine Venner, dersom I gøre, hvad jeg befaler eder.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 Jeg kalder eder ikke længere Tjenere; thi Tjeneren ved ikke, hvad hans Herre gør; men eder har jeg kaldt Venner; thi alt det, som jeg har hørt af min Fader, har jeg kundgjort eder.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 I have ikke udvalgt mig, men jeg har udvalgt eder og sat eder til, at I skulle gå hen og bære Frugt, og eders Frugt skal blive ved, for at Faderen skal give eder, hvad som helst I bede ham om i mit Navn.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 Dette befaler jeg eder, at I skulle elske hverandre.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 Når Verden hader eder, da vid, at den har hadet mig førend eder.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 Vare I af Verden, da vilde Verden elske sit eget; men fordi I ikke ere af Verden, men jeg har valgt eder ud af Verden, derfor hader Verden eder.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Kommer det Ord i Hu, som jeg har sagt eder: En Tjener er ikke større end sin Herre. Have de forfulgt mig, ville de også forfølge eder; have de holdt mit Ord, ville de også holde eders.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 Men alt dette ville de gøre imod eder for mit Navns Skyld, fordi de ikke kende den, som sendte mig.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 Dersom jeg ikke var kommen og havde talt til dem, havde de ikke Synd; men nu have de ingen Undskyldning for deres Synd.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 Den, som hader mig, hader også min Fader.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 Havde jeg ikke gjort de Gerninger iblandt dem, som ingen anden har gjort, havde de ikke Synd; men nu have de set dem og dog hadet både mig og min Fader.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 Dog, det Ord, som er skrevet i deres Lov, må opfyldes: De hadede mig uforskyldt.
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 Men når Talsmanden kommer, som jeg skal sende eder fra Faderen, Sandhedens Ånd, som udgår fra Faderen, da skal han vidne om mig.
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 Men også I skulle vidne; thi I vare med mig fra Begyndelsen."
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

< Johannes 15 >