< Johannes 13 >
1 Men før Påskehøjtiden, da Jesus vidste, at hans Time var kommen, til at han skulde gå bort fra denne Verden til Faderen, da, ligesom han havde elsket sine egne, som vare i Verden, så elskede han dem indtil Enden.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 Og medens der holdtes Aftensmåltid, da Djævelen allerede havde indskudt i Judas's, Simons Søns, Iskariots Hjerte, at han skulde forråde ham;
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 da Jesus vidste, at Faderen havde givet ham alle Ting i Hænde, og at han var udgået fra Gud og gik hen til Gud:
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 så rejser han sig fra Måltidet og lægger sine Klæder fra sig, og han tog et Linklæde og bandt det om sig.
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Derefter hælder han Vand i Vaskefadet og begyndte at to Disciplenes Fødder og at tørre dem med Linklædet, som han var ombunden med.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 Han kommer da til Simon Peter; og denne siger til ham: "Herre! tor du mine Fødder?"
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 Jesus svarede og sagde til ham: "Hvad jeg gør, ved du ikke nu, men du skal forstå det siden efter."
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 Peter siger til ham: "Du skal i al Evighed ikke to mine Fødder." Jesus svarede ham: "Dersom jeg ikke tor dig, har du ikke Lod sammen med mig." (aiōn )
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn )
9 Simon Peter siger til ham: "Herre! ikke mine Fødder alene, men også Hænderne og Hovedet."
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 Jesus siger til ham: "Den, som er tvættet, har ikke nødig at to andet end Fødderne, men er ren over det hele; og I ere rene, men ikke alle."
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 Thi han kendte den, som forrådte ham; derfor sagde han: "I ere ikke alle rene."
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 Da han nu havde toet deres Fødder og havde taget sine Klæder og atter sat sig til Bords, sagde han til dem: "Vide I, hvad jeg har gjort ved eder?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 I kalde mig Mester og Herre, og I tale ret, thi jeg er det.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 Når da jeg, Herren og Mesteren, har toet eders Fødder, så ere også I skyldige at to hverandres Fødder.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 Thi jeg har givet eder et Eksempel, for at, ligesom jeg gjorde ved eder, skulle også I gøre.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, en Tjener er ikke større end sin Herre, ikke heller et Sendebud større end den, som har sendt ham.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 Når I vide dette, ere I salige, om I gøre det.
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 Jeg taler ikke om eder alle; jeg ved, hvilke jeg har udvalgt; men Skriften måtte opfyldes: Den, som æder Brødet med mig, har opløftet sin Hæl imod mig.
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 Fra nu af siger jeg eder det, førend det sker, for at I, når det er sket, skulle tro, at det er mig.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, den, som modtager, hvem jeg sender, modtager mig; men den, som modtager mig, modtager ham, som har sendt mig."
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 Da Jesus havde sagt dette, blev han heftigt bevæget i Ånden og vidnede og sagde: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, en af eder vil forråde mig."
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Da så Disciplene på hverandre, tvivlrådige om, hvem han talte om.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 Men der var en iblandt hans Disciple, som sad til Bords ved Jesu Side, han, hvem Jesus elskede.
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 Til denne nikker da Simon Peter og siger til ham: "Sig, hvem det er, han taler om?"
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 Men denne bøjer sig op til Jesu Bryst og siger til ham: "Herre! hvem er det?"
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 Jesus svarer: "Det er den, hvem jeg giver det Stykke Brød, som jeg dypper." Så dypper han Stykket og tager og giver det til Judas, Simons Søn, Iskariot.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 Og efter at han havde fået Stykket, da gik Satan ind i ham. Så siger Jesus til ham: "Hvad du gør, gør det snart!"
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 Men ingen af dem, som sade til Bords, forstod, hvorfor han sagde ham dette.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 Thi nogle mente, efterdi Judas havde Pungen, at Jesus sagde til ham: "Køb, hvad vi have nødig til Højtiden;" eller at han skulde give noget til de fattige.
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 Da han nu havde fået Stykket, gik han straks ud. Men det var Nat.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 Da han nu var gået ud, siger Jesus: "Nu er Menneskesønnen herliggjort, og Gud er herliggjort i ham.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 Dersom Gud er herliggjort i ham, skal Gud også herliggøre ham i sig, og han skal snart herliggøre ham.
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 Børnlille! endnu en liden Stund er jeg hos eder. I skulle lede efter mig, og ligesom jeg sagde til Jøderne: "Hvor jeg går hen, kunne I ikke komme," siger jeg nu også til eder.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 Jeg giver eder en ny Befaling, at I skulle elske hverandre, at ligesom jeg elskede eder, skulle også I elske hverandre.
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 Derpå skulle alle kende, at I ere mine Disciple, om I have indbyrdes Kærlighed."
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 Simon Peter siger til ham: "Herre! hvor går du hen?" Jesus svarede ham: "Hvor jeg går hen, kan du ikke nu følge mig, men siden skal du følge mig."
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 Peter siger til ham: "Herre! hvorfor kan jeg ikke følge dig nu? Jeg vil sætte mit Liv til for dig?
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 Jesus svarer: "Vil du sætte dit Liv til for mig? Sandelig, sandelig, siger jeg dig, Hanen skal ikke gale, førend du har fornægtet mig tre Gange."
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!