< Johannes 12 >

1 Seks Dage før Påske kom Jesus nu til Bethania, hvor Lazarus boede, han, som Jesus havde oprejst fra de døde.
Kwana shidda kafin idin ketarewa, Yesu ya zo Baitanya inda Li'azaru yake, wato wannan da Yesu ya tada daga matattu.
2 Der gjorde de da et Aftensmåltid for ham, og Martha vartede op; men Lazarus var en af dem, som sade til Bords med ham.
Sai suka shirya masa abinci a wurin kuma Matta ce ke hidima, Li'azaru kuwa ya kasance cikin wadanda ke kan tebiri tare da Yesu.
3 Da tog Maria et Pund af ægte, såre kostbar Nardussalve og salvede Jesu Fødder og tørrede hans Fødder med sit Hår; og Huset blev fuldt af Salvens Duft.
Sai Maryamu ta dauki wani turare da aka yi da man nard, ta shafe kafafun Yesu da shi, ta kuma share kafafun nasa da gashin kanta. Sai gida ya cika da kamshin turaren.
4 Da siger en af hans Disciple, Judas, Simons Søn, Iskariot, han, som siden forrådte ham:
Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin almajiransa, wanda zai bashe shi, ya ce, “
5 "Hvorfor blev denne Salve ikke solgt for tre Hundrede Denarer og given til fattige?"
“Me yasa ba a sayar da wannan turare dinari dari uku a ba gajiyayyu ba?”
6 Men dette sagde han, ikke fordi han brød sig om de fattige, men fordi han var en Tyv og havde Pungen og bar, hvad der blev lagt deri.
Ya fadi haka ba don ya damu da gajiyayyu ba, amma domin shi barawo ne: shi ne ma'aji, kuma yana sata daga jakkar kudi.
7 Da sagde Jesus: "Lad hende med Fred, hun har jo bevaret den til min Begravelsesdag!
Yesu ya ce, “Ku kyale ta ta ajiye abinda ta tanada domin jana'iza ta.
8 De fattige have I jo altid hos eder; men mig have I ikke altid."
Gajiyayyu suna tare da ku a koyaushe, ni kuwa ba zan kasance da ku koyaushe ba.
9 En stor Skare af Jøderne fik nu at vide, at han var der; og de kom ikke for Jesu Skyld alene, men også for at se Lazarus, hvem han havde oprejst fra de døde.
To babban taron Yahudawa sun ji cewa Yesu yana wurin, sai suka zo, ba don Yesu kawai ba amma domin su ga Li'azaru, wanda Yesu ya tada daga matattu.
10 Men Ypperstepræsterne rådsloge om også at slå Lazarus ihjel:
Sai manyan firistoci suka kulla makirci akan yadda za su kashe Li'azaru shima;
11 thi for hans Skyld gik mange af Jøderne hen og troede på Jesus.
domin saboda shi ne yahudawa dayawa suka je suka bada gaskiya ga Yesu.
12 Den følgende Dag, da den store Skare, som var kommen til Højtiden, hørte, at Jesus kom til Jerusalem,
Kashegari, babban taro suka zo idin. Da suka ji cewa Yesu na zuwa Urushalima,
13 toge de Palmegrene og gik ud imod ham og råbte: "Hosanna! velsignet være den, som kommer, i Herrens Navn, Israels Konge!"
Sai suka dauki ganyen dabino suka fita gari suka tare shi da kira mai karfi suna cewa, “Hosanna! Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila.
14 Men Jesus fandt et ungt Æsel og satte sig derpå, som der er skrevet:
Yesu ya sami wani Aholakin jaki, ya hau kansa; kamar yadda aka rubuta,
15 "Frygt ikke, Zions Datter! se, din Konge kommer, siddende på en Asenindes Føl."
“Kada ki ji tsoro ke 'yar Sihiyona; duba, ga Sarkinki na zuwa, zaune a kan danJaki”.
16 Dette forstode hans Disciple ikke først; men da Jesus var herliggjort, da kom de i Hu, at dette var skrevet om ham, og at de havde gjort dette for ham.
Almajiransa basu fahimci wannan al'amari ba da farko, amma bayan da aka daukaka Yesu, sai suka tuna cewa an rubuta wadannan abubuwa game da shi, kuma sun yi masa wadannan abubuwa.
17 Skaren, som var med ham, vidnede nu, at han havde kaldt Lazarus frem fra Graven og oprejst ham fra de døde.
Sai taron da ke tare da Yesu a ranar da ya kira Li'azaru daga kabari ya kuma tashe shi daga matattu, suka bada shaida.
18 Det var også derfor, at Skaren gik ham i Møde, fordi de havde hørt, at han havde gjort dette Tegn.
Domin wannan ne kuma taron suka zo domin su sadu da shi saboda sun ji cewa ya yi wannan alama.
19 Da sagde Farisæerne til hverandre: "I se, at I udrette ikke noget; se, Alverden går efter ham."
Don haka, sai farisawa suka shiga magana a tsakanin su suna cewa “Duba, babu abinda zaku iya yi; kun ga, duniya ta gama bin sa.
20 Men der var nogle Grækere af dem, som plejede at gå op for at tilbede på Højtiden.
Akwai wadansu Helinawa cikin wadanda suka je sujada a idin.
21 Disse gik nu til Filip, som var fra Bethsajda i Galilæa, og bade ham og sagde: "Herre! vi ønske at se Jesus."
Wadannan suka tafi wurin filibus, mutumin Betsaida da ke Galili, suka ce masa, “Mallam, muna so mu ga Yesu.
22 Filip kommer og siger det til Andreas, Andreas og Filip komme og sige det til Jesus.
Filibus ya tafi ya fadawa Andrawus; sai Andrawus ya tafi tare da Filibus, suka kuwa gaya wa Yesu.
23 Men Jesus svarede dem og sagde: "Timen er kommen, til at Menneskesønnen skal herliggøres.
Yesu ya amsa masu ya ce, “sa'a ta zo da za'a daukaka Dan mutum.
24 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, hvis ikke Hvedekornet falder i Jorden og dør, bliver det ene; men dersom det dør, bærer det megen Frugt.
Hakika, hakika, Ina ce maku, in ba kwayar alkama ta fadi kasa ba ta mutu, za ta kasance ita kadai; amma idan ta mutu, za ta bada 'ya'ya masu yawa.
25 Den, som elsker sit Liv, skal miste det; og den, som hader sit Liv i denne Verden, skal bevare det til et evigt Liv. (aiōnios g166)
Duk wanda yake son ransa, zai rasa shi; amma wanda ba ya son ransa a duniyan nan za ya kiyaye shi domin rayuwa ta har abada. (aiōnios g166)
26 Om nogen tjener mig, han følge mig, og hvor jeg er, der skal også min Tjener være; om nogen tjener mig, ham skal Faderen ære.
Idan wani na bauta mani, to bari ya biyo ni; kuma duk inda nike, a can bawana zai kasance kuma. Duk wanda ke bauta mani, Uban zai girmama shi.
27 Nu er min Sjæl forfærdet; og hvad skal jeg sige? Fader, frels mig fra denne Time? Dog, derfor er jeg kommen til denne Time.
Yanzu raina na cikin damuwa, to me zan ce? 'Uba, ka cece ni daga wannan sa'a? Amma Saboda wannan dalili ne na zo wannan sa'a.
28 Fader herliggør dit Navn!" Da kom der en Røst fra Himmelen: "Både har jeg herliggjort det, og vil jeg atter herliggøre det."
Uba, ka daukaka sunanka”. Sai wata murya daga sama ta ce, “Na daukaka shi, zan kuma sake daukaka shi.
29 Da sagde Skaren, som stod og hørte det, at det havde tordnet; andre sagde: "En Engel har talt til ham."
Daganan sai taron dake tsaye kuma suka ji muryar, suka ce an yi tsawa. Wasu suka ce, “Mala'ika ya yi magana da shi”.
30 Jesus svarede og sagde: "Ikke for min Skyld er denne Røst kommen, men for eders Skyld.
Yesu ya amsa ya ce, “wannnan murya ta zo ba saboda ni ba, amma domin ku.”
31 Nu går der Dom over denne Verden, nu skal denne Verdens Fyrste kastes ud,
Yanzu za'a shar'anta duniya. Yanzu za'a kori mai mulkin duniyan nan.
32 og jeg skal, når jeg bliver ophøjet fra Jorden, drage alle til mig."
Sa, annan ni, idan an daga ni daga duniya, zan jawo dukan mutane zuwa gare ni”.
33 Men dette sagde han for at betegne, hvilken Død han skulde dø.
Ya fadi wannan ne domin ya nuna irin mutuwar da za ya yi.
34 Skaren svarede ham: "Vi have hørt af Loven, at Kristus bliver evindelig, og hvorledes siger da du, at Menneskesønnen bør ophøjes? Hvem er denne Menneskesøn?" (aiōn g165)
Taro suka amsa masa cewa, “Mun ji a cikin shari'a cewa Almasihu za ya kasance har abada. Yaya za ka ce, 'za'a daga dan mutum'? Wanene wannan dan mutum?” (aiōn g165)
35 Da sagde Jesus til dem: "Endnu en liden Tid er Lyset hos eder. Vandrer, medens I have Lyset, for at Mørke ikke skal overfalde eder! Og den, som vandrer i Mørket, ved ikke, hvor han går hen.
Yesu ya ce masu, “Nan da lokaci kadan za ku kasance da haske, ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya mamaye ku. Wanda ke tafiya cikin duhu, bai san inda za shi ba.
36 Medens I have Lyset, tror på Lyset, for at I kunne blive Lysets Børn!" Dette talte Jesus, og han gik bort og blev skjult for dem.
Ku gaskata ga haske tun yana tare da ku domin ku zama yayan haske”. Yesu ya fadi wadannan abubuwa sannan ya tafi ya boye masu.
37 Men endskønt han havde gjort så mange Tegn for deres Øjne, troede de dog ikke på ham,
Kodashike Yesu ya yi alamu da dama a gabansu, duk da haka ba su gaskata shi ba.
38 for at Profeten Esajas's Ord skulde opfyldes, som han har sagt: "Herre! hvem troede det, han hørte af os, og for hvem blev Herrens Arm åbenbaret?"
Saboda maganar annabi Ishaya ta cika, wadda ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata rahoton mu? Ga wa kuma hannun Ubangiji ya bayyana?
39 Derfor kunde de ikke tro, fordi Esajas har atter sagt:
Saboda wannan dalili basu gaskata ba, gama Ishaya ya sake cewa,
40 "Han har blindet deres Øjne og forhærdet deres Hjerte, for at de ikke skulle se med Øjnene og forstå med Hjertet og omvende sig, så jeg kunde helbrede dem."
ya makantar da su, ya kuma taurare zuciyarsu, saboda kada su gani da idanunsu, su kuma sami fahimta da zuciyarsu, su juyo wurina in warkar da su.
41 Dette sagde Esajas, fordi han så hans Herlighed og talte om ham.
Ishaya ya fadi wadannan abubuwa ne domin ya hangi daukakar Yesu ya kuma yi magana game da shi.
42 Alligevel var der dog mange, endogså af Rådsherrerne, som troede på ham; men for Farisæernes Skyld bekendte de det ikke, for at de ikke skulde blive udelukkede af Synagogen;
Amma duk da haka, dayawa cikin shugabanni suka gaskata Yesu. Amma saboda farisawa, basu shaida shi a sarari ba, domin kada a kore su daga majami'a.
43 thi de elskede Menneskenes Ære mere end Guds Ære.
Suna son yabo daga mutane fiye da yabon dake zuwa daga Allah.
44 Men Jesus råbte og sagde: "Den, som tror på mig, tror ikke på mig, men på ham, som sendte mig,
Yesu ya yi magana da babbar murya, ya ce, “Wanda ya gaskata ni, ba ni yake gaskatawa kadai ba, amma kuma yana gaskata wanda ya aiko ni,
45 og den, som ser mig, ser den, som sendte mig.
kuma wanda ke gani na, yana ganin shi wanda ya aiko ni.
46 Jeg er kommen som et Lys til Verden, for at hver den, som tror på mig, ikke skal blive i Mørket.
Na zo ne a matsayin haske a duniya, saboda duk wanda ya gaskata da ni ba za ya yi tafiya cikin duhu ba.
47 Og om nogen hører mine Ord og ikke vogter på dem, ham dømmer ikke jeg; thi jeg er ikke kommen for at dømme Verden, men for at frelse Verden.
Duk wanda ya ji maganata baya gaskata ba, ba ni hukunta shi; gama ban zo in yi wa duniya hukunci ba, amma don in ceci duniya.
48 Den, som foragter mig og ikke modtager mine Ord, har den, som dømmer ham; det Ord, som jeg har talt, det skal dømme ham på den yderste Dag.
Wanda ya ki ni, ya kuma ki ya karbi magana ta, akwai wanda za ya yi masa hukunci. Kalmar da na fada, ita ce za ta yi masa hukunci a rana ta karshe.
49 Thi jeg har ikke talt af mig selv; men Faderen, som sendte mig, han har givet mig Befaling om, hvad jeg skal sige, og hvad jeg skal tale.
Maganar da ni ke yi, ba ra'ayina ba ne. Amma Uba wanda ya aiko ni shi ke bani umarni game da abin da zan ce da abin da zan fadi.
50 Og jeg ved, at hans Befaling er evigt Liv. Altså, hvad jeg taler, taler jeg således, som Faderen har sagt mig." (aiōnios g166)
Na san umarninsa rai ne madawwami, don haka na ce - kamar yadda Uba ya fada, haka ni ma nake fadi.” (aiōnios g166)

< Johannes 12 >