< Johannes 11 >

1 Men der lå en Mand syg, Lazarus fra Bethania, den Landsby, hvor Maria og hendes Søster Martha boede.
To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
2 Men Maria var den, som salvede Herren med Salve og tørrede hans Fødder med sit Hår; hendes Broder Lazarus var syg.
Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
3 Da sendte Søstrene Bud til ham og lod sige: "Herre! se, den, du elsker, er syg."
Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
4 Men da Jesus hørte dette, sagde han: "Denne Sygdom er ikke til Døden, men for Guds Herligheds Skyld, for at Guds Søn skal herliggøres ved den."
Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
5 Men Jesus elskede Martha og hendes Søster og Lazarus.
Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
6 Da han nu hørte, at han var syg, blev han dog to Dage på det Sted, hvor han var.
Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
7 Derefter siger han så til Disciplene:"Lader os gå til Judæa igen!
Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
8 Disciplene sige til ham: "Rabbi! nylig søgte Jøderne at stene dig, og du drager atter derhen?"
Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
9 Jesus svarede: "Har Dagen ikke tolv Timer? Vandrer nogen om Dagen, da støder han ikke an; thi han ser denne Verdens Lys.
Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
10 Men vandrer nogen om Natten, da støder han an; thi Lyset er ikke i ham."
Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
11 Dette sagde han, og derefter siger han til dem: "Lazarus, vor Ven, er sovet ind; men jeg går hen for at vække ham af Søvne."
Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
12 Da sagde Disciplene til ham: "Herre! sover han, da bliver han helbredt."
Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
13 Men Jesus havde talt om hans Død; de derimod mente, at han talte om Søvnens Hvile.
Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
14 Derfor sagde da Jesus dem rent ud: "Lazarus er død!
Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
15 Og for eders Skyld er jeg glad over, at jeg ikke var der, for at I skulle tro; men lader os gå til ham!"
amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
16 Da sagde Thomas (hvilket betyder Tvilling), til sine Meddisciple: "Lader os også gå, for at vi kunne dø med ham!"
Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
17 Da Jesus nu kom, fandt han, at han havde ligget i Graven allerede fire Dage.
Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
18 Men Bethania var nær ved Jerusalem, omtrent femten Stadier derfra.
Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
19 Og mange af Jøderne vare komne til Martha og Maria for at trøste dem over deres Broder.
Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
20 Da Martha nu hørte, at Jesus kom, gik hun ham i Møde; men Maria blev siddende i Huset.
Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
21 Da sagde Martha til Jesus: "Herre! havde du været her, da var min Broder ikke død.
Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
22 Men også nu ved jeg, at hvad som helst du beder Gud om, vil Gud give dig."
Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
23 Jesus siger til hende: "Din Broder skal opstå."
Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
24 Martha siger til ham: "Jeg ved at han skal opstå i Opstandelsen på den yderste Dag."
Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
25 Jesus sagde til hende: "Jeg er Opstandelsen og Livet; den, som tror på mig, skal leve, om han end dør.
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
26 Og hver den, som lever og tror på mig, skal i al Evighed ikke dø. Tror du dette?" (aiōn g165)
kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn g165)
27 Hun siger til ham: "Ja, Herre! jeg tror, at du er Kristus, Guds Søn, den, som kommer til Verden."
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
28 Og da hun havde sagt dette, gik hun bort og kaldte hemmeligt sin Søster Maria og sagde: "Mesteren er her og kalder ad dig."
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
29 Da hun hørte det, rejste hun sig hastigt og gik til ham.
Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
30 Men Jesus var endnu ikke kommen til Landsbyen, men var på det Sted, hvor Martha havde mødt ham.
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
31 Da nu Jøderne, som vare hos hende i Huset og trøstede hende, så, at Maria stod hastigt op og gik ud, fulgte de hende, idet de mente, at hun gik ud til Graven for at græde der.
Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
32 Da Maria nu kom derhen, hvor Jesus var, og så ham, faldt hun ned for hans Fødder og sagde til ham: "Herre! havde du været her da var min Broder ikke død."
Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
33 Da nu Jesus så hende græde og så Jøderne, som vare komne med hende, græde, harmedes han i Ånden og blev heftig bevæget i sit Indre; og han sagde:
Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
34 "Hvor have I lagt ham?" De sige til ham: "Herre! kom og se!"
Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
35 Jesus græd.
Yesu ya yi kuka.
36 Da sagde Jøderne: "Se, hvor han elskede ham!"
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
37 Men nogle af dem sagde: "Kunde ikke han, som åbnede den blindes Øjne, have gjort, at også denne ikke var død?"
Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
38 Da harmes Jesus atter i sit Indre og går hen til Graven. Men det var en Hule, og en Sten lå for den.
Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
39 Jesus siger: "Tager Stenen bort!" Martha, den dødes Søster, siger til ham: "Herre! han stinker allerede; thi han har ligget der fire Dage:"
Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
40 Jesus siger til hende: " Sagde jeg ikke, at dersom du tror, skal du se Guds Herlighed?"
Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
41 Da toge de Stenen bort. Men Jesus opløftede sine Øjne og sagde: "Fader! jeg takker dig, fordi du har hørt mig.
Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
42 Jeg vidste vel, at du altid hører mig; men for Skarens Skyld, som står omkring, sagde jeg det, for at de skulle tro, at du har udsendt mig."
Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
43 Og da han havde sagt dette, råbte han med høj Røst: "Lazarus, kom herud!"
Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
44 Og den døde kom ud, bunden med Jordeklæder om Fødder og Hænder, og et Tørklæde var bundet om hans Ansigt, Jesus siger til dem: "Løser ham, og lader ham gå!"
Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
45 Mange af de Jøder, som vare komne til Maria og havde set, hvad han havde gjort, troede nu på ham;
Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
46 men nogle af dem gik hen til Farisæerne og sagde dem, hvad Jesus, havde gjort.
Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
47 Ypperstepræsterne og Farisæerne sammenkaldte da et Møde af Rådet og sagde: "Hvad gøre vi? thi dette Menneske gør mange Tegn.
Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
48 Dersom vi lade ham således blive ved, ville alle tro på ham, og Romerne ville komme og tage både vort Land og Folk."
In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
49 Men en af dem, Kajfas, som var Ypperstepræst i det År, sagde til dem:
Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
50 "I vide intet; ej heller betænke I, at det er os gavnligt, at eet Menneske dør for Folket, og at ikke det hele Folk skal gå til Grunde."
Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
51 Men dette sagde han ikke af sig selv; men da han var Ypperstepræst i det År, profeterede han at Jesus skulde dø for Folket;
Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
52 og ikke for Folket alene, men for at han også kunde samle Guds adspredte Børn sammen til eet.
ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
53 Fra den Dag af rådsloge de derfor om at ihjelslå ham.
Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
54 Derfor vandrede Jesus ikke mere frit om iblandt jøderne, men gik bort derfra ud på Landet, nær ved Ørkenen, til en By, som kaldes Efraim; og han blev der med sine Disciple.
Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
55 Men Jødernes Påske var nær; og mange fra Landet gik op til Jerusalem før Påsken for at rense sig.
Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
56 Da ledte de efter Jesus og sagde mellem hverandre, da de stode i Helligdommen: "Hvad mene I? Mon han ikke kommer til Højtiden?"
Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
57 Men Ypperstepræsterne og Farisæerne havde givet Befaling om at dersom nogen vidste, hvor han var, skulde han give det til Kende for at de kunde gribe ham.
Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.

< Johannes 11 >