< Joel 3 >

1 Thi se, i de Dage og på den Tid, når jeg vender Judas og Jerusalems Skæbne,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 samler jeg alle Hedningefolk og fører dem ned i Josafats Dal. Der vil jeg holde Rettergang med dem om mit Folk og min Arvelod Israel, som de spredte blandt Folkene; og de delte mit Land,
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 kastede Lod om mit Folk, gav en Dreng for en Skøge og solgte en Pige for Vin, som de drak.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 Og desuden, hvad vil I mig, Tyrus og Zidon og alle Filisterlands Kredse? Er der noget, I vil gengælde mig, eller vil I gøre mig noget? Hastigt og brat lader jeg Gengældelse komme over eders Hoved,
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 I, som tog mit Sølv og Guld, bortførte mine kostbareste Ting til eders Borge
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 og solgte Judæerne og Jerusalems Borgere til Grækerne, for at de skulde føres langt bort fra deres Hjem.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Se, jeg vækker dem op fra det Sted, I solgte dem til, og lader Gengældelse komme over eders Hoved.
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 Jeg sælger eders Sønner og Døtre til Judæerne, og de skal sælge dem til Sabæerne, Folket i det fjerne Land, så sandt HERREN har talet.
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Råb det ud blandt Folkene, helliger en Krig, væk Heltene op! Lad alle våbenføre Mænd komme og drage op!
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Smed eders Plovjern om til Sværd, eders Vingårdsknive til Spyd! Svæklingen skal sige: "Jeg er en Helt!"
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Skynd eder og kom, alle Hedningefolk viden om, og saml eder! Før dine Helte derned, HERRE!
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 Hedningefolkene skal vækkes op og drage til Josafats Dal; thi der vil jeg sidde til Doms over alle Hedningefolk viden om.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Sving Seglen, thi Høsten er moden; kom og stamp, thi Persekummen er fuld! Persekarrene løber over, thi stor er Folkenes Ondskab.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Skarer på Skarer i Opgørets Dal! Thi nær er HERRENs Dag i Opgørets Dal.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 Sol og Måne sortner, og Stjernerne mister deres Glans.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 HERREN brøler fra Zion, fra Jerusalem løfter han sin Røst; Himmelen og Jorden skælver. Men HERREN er Ly for sit Folk og Værn for Israels Børn.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 Og I skal kende, at jeg er HERREN eders Gud, som bor på Zion, mit hellige Bjerg. Jerusalem skal blive en Helligdom, og fremmede skal ikke mere drage derigennem.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 På hin Dag skal Bjergene dryppe af Most og Højene flyde med Mælk; alle Judas Bække skal strømme med Vand, og en kilde skal vælde frem fra HERRENs Hus og vande Akaciedalen.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 Ægypten skal blive øde, Edom en øde Ørk for deres Vold mod Judæerne, i hvis Land de udgød uskyldigt Blod.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 Og Juda skal være beboet evindelig, Jerusalem fra Slægt til Slægt.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 Jeg hævner deres Blod, som jeg endnu ikke har hævnet; og HERREN bor på Zion.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Joel 3 >