< Job 8 >

1 Så tog Sjuhiten Bildad til Orde og sagde:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 "Hvor længe taler du så, hvor længe skal Mundens Uvejr rase?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Mon Gud vel bøjer Retten, bøjer den Almægtige Retfærd?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 Har dine Sønner syndet imod ham, og gav han dem deres Brøde i Vold,
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 så søg du nu hen til Gud og bed hans Almagt om Nåde!
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 Såfremt du er ren og oprigtig, ja, da vil han våge over dig, genrejse din Retfærds Bolig;
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 din fordums Lykke vil synes ringe, såre stor skal din Fremtid blive.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Thi spørg dog den befarne Slægt, læg Mærke til Fædrenes Granskning!
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 Vi er fra i Går, og intet ved vi, en Skygge er vore Dage på Jord.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Mon ej de kan lære dig, sige dig det og give dig Svar af Hjertet:
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Vokser der Siv, hvor der ikke er Sump, gror Nilgræs frem, hvor der ikke er Vand?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 Endnu i Grøde, uden at høstes, visner det før alt andet Græs.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Så går det enhver, der glemmer Gud, en vanhelliges Håb slår fejl:
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 som Sommerspind er hans Tilflugt, hans Tillid er Spindelvæv;
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 han støtter sig til sit Hus, det falder, han klynger sig til det, ej står det fast.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 I Solskinnet vokser han frodigt, hans Ranker breder sig Haven over,
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 i Stendynger fletter hans Rødder sig ind, han hager sig fast mellem Sten;
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 men rives han bort fra sit Sted, fornægter det ham: "Jeg har ikke set dig!"
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Se, det er Glæden, han har af sin Vej, og af Jorden fremspirer en anden!
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Se, Gud agter ej den uskyldige ringe, han holder ej fast ved de ondes Hånd.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 End skal han fylde din Mund med Latter og dine Læber med Jubel;
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 dine Avindsmænd skal klædes i Skam og gudløses Telt ej findes mer!
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >