< Job 36 >
2 Bi nu lidt, jeg har noget at sige dig, thi end har jeg Ord til Forsvar for Gud.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Jeg vil hente min Viden langvejsfra og skaffe min Skaber Ret;
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 thi for vist, mine Ord er ikke Opspind, en Mand med fuldkommen Indsigt har du for dig.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Se, Gud forkaster det stive Sind,
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 den gudløse holder han ikke i Live; de arme lader han få deres Ret,
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 fra retfærdige vender han ikke sit Blik, men giver dem Plads for stedse hos Konger på Tronen i Højhed.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Og hvis de bindes i Lænker, fanges i Nødens Bånd,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 så viser han dem deres Gerning, deres Synder, at de hovmodede sig,
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 åbner deres Øre for Tugt og byder dem vende sig bort fra det onde.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 Hvis de så hører og bøjer sig, da ender de deres Dage i Lykke, i liflig Fryd deres År.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Men hører de ikke, falder de for Sværd og opgiver Ånden i Uforstand.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Men vanhellige Hjerter forbitres; når han binder dem, råber de ikke om Hjælp;
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 i Ungdommen dør deres Sjæl, deres Liv får Mandsskøgers Lod.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Den elendige frelser han ved hans Elende og åbner hans Øre ved Trængsel.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Men dig har Medgangen lokket, du var i Fred for Ulykkens Gab; ingen Trængsel indjog dig Skræk, fuldt var dit Bord af fede Retter.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Den gudløses som kom til fulde over dig, hans retfærdige Dom greb dig fat.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Lad dig ikke lokke af Vrede til Spot eller Bødens Storhed lede dig vild!
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Kan vel dit Skrig gøre Ende på Nøden, eller det at du opbyder al din Kraft?
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Ej må du længes efter Natten, som. opskræmmer Folkeslag der, hvor de er;
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 var dig og vend dig ikke til Uret, så du foretrækker ondt for at lide.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Se, ophøjet er Gud i sin Vælde, hvo er en Lærer som han?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Hvo foreskrev ham hans Vej, og hvo turde sige: "Du gjorde Uret!"
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Se til at ophøje hans Værk, som Mennesker priser i Sang!
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Alle Mennesker ser det med Fryd, skønt dødelige skuer det kun fra det fjerne.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Se, Gud er ophøjet, kan ikke ransages, Tal på hans År kan ikke fides.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Thi Dråber drager han ud af Havet, i hans Tåge siver de ned som Regn,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 og Skyerne lader den strømme og dryppe på mange Folk.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Hvo fatter mon Skyernes Vidder eller hans Boligs Bulder?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Se, han breder sin Tåge om sig og skjuler Havets Rødder;
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Thi dermed nærer han Folkene, giver dem Brød i Overflod;
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 han hyller sine Hænder i Lys og sender det ud imod Målet;
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 hans Torden melder hans Komme, selv Kvæget melder hans Optræk.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.