< Job 32 >

1 Da nu hine tre Mænd ikke mere svarede Job, fordi han var retfærdig i sine egne Øjne,
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 blussede Vreden op i Buziten Elihu, Barak'els Søn, af Rams Slægt. På Job vrededes han, fordi han gjorde sig retfærdigere end Gud,
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 og på hans tre Venner, fordi de ikke fandt noget Svar og dog dømte Job skyldig.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Elihu havde ventet, så længe de talte med Job, fordi de var ældre end han;
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 men da han så, at de tre Mænd intet havde at svare, blussede hans Vrede op;
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 og Buziten Elihu, Barak'els Søn, tog til Orde og sagde: Ung af Dage er jeg, og I er gamle Mænd, derfor holdt jeg mig tilbage, angst for at meddele eder min Viden;
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 jeg tænkte: "Lad Alderen tale og Årenes Mængde kundgøre Visdom!"
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Dog Ånden, den er i Mennesket, og den Almægtiges Ånde giver dem Indsigt;
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 de gamle er ikke altid de kloge, Oldinge ved ej altid, hvad Ret er;
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 derfor siger jeg: Hør mig, lad også mig komme frem med min Viden!
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Jeg biede på, at I skulde tale, lyttede efter forstandige Ord, at I skulde finde de rette Ord;
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 jeg agtede nøje på eder; men ingen af eder gendrev Job og gav Svar på hans Ord.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Sig nu ikke: "Vi stødte på Visdom, Gud må fælde ham, ikke et Menneske!"
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Mod mig har han ikke rettet sin Tale, og med eders Ord vil jeg ikke svare ham.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 De blev bange, svarer ej mer, for dem slap Ordene op.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 Skal jeg tøve, fordi de tier og står der uden at svare et Ord?
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 Også jeg vil svare min Del, også jeg vil frem med min Viden!
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Thi jeg er fuld af Ord, Ånden i mit Bryst trænger på;
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 som tilbundet Vin er mit Bryst, som nyfyldte Vinsække nær ved at sprænges;
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 tale vil jeg for at få Luft, åbne mine Læber og svare.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Forskel gør jeg ikke og smigrer ikke for nogen;
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 thi at smigre bruger jeg ikke, snart rev min Skaber mig ellers bort!
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.

< Job 32 >