< Job 19 >
1 Så tog Job til Orde og svarede:
Sai Ayuba ya amsa,
2 "Hvor længe vil I krænke min Sjæl og slå mig sønder med Ord?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 I håner mig nu for tiende Gang, mishandler mig uden Skam.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Har jeg da virkelig fejlet, hænger der Fejl ved mig?
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Eller gør I jer store imod mig og revser mig ved at smæde?
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Så vid da, at Gud har bøjet min Ret, omspændt mig med sit Net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Se, jeg skriger: Vold! men får ikke Svar, råber om Hjælp, der er ingen Ret.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Han spærred min Vej, jeg kom ikke frem, han hylled mine Stier i Mørke;
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 han klædte mig af for min Ære, berøved mit Hoved Kronen,
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 brød mig ned overalt, så jeg må bort, oprykked mit Håb som Træet;
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 hans Vrede blussede mod mig, han regner mig for sin Fjende;
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 samlede rykker hans Flokke frem og bryder sig Vej imod mig, de lejrer sig om mit Telt.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Mine Brødre har fjernet sig fra mig, Venner er fremmede for mig,
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 mine nærmeste og Hendinge holder sig fra mig, de, der er i mit Hus, har glemt mig;
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 mine Piger regner mig for en fremmed, vildfremmed er jeg i deres Øjne;
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 ej svarer min Træl, når jeg kalder, jeg må trygle ham med min Mund;
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 ved min Ånde væmmes min Hustru, mine egne Brødre er jeg en Stank;
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 selv Drenge agter mig ringe, når jeg reljser mig, taler de mod mig;
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Standsfælleræmmes til Hobe ved mig, de, jeg elskede, vender sig mod mig.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Benene hænger fast ved min Hud, med Kødet i Tænderne slap jeg bort.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Nåde, mine Venner, Nåde, thi Guds Hånd har rørt mig!
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Hvi forfølger og I mig som Gud og mættes ej af mit Kød?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Ak, gid mine Ord blev skrevet op, blev tegnet op i en Bog,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 med Griffel af Jern, med Bly indristet i Hlippen for evigt!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Men jeg ved, at min Løser lever, over Støvet vil en Forsvarer stå frem.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 Når min sønderslidte Hud er borte, skal jeg ud fra mit Kød skue Gud,
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 hvem jeg skal se på min Side; ham skal mine Øjne se, ingen fremmed! Mine Nyrer forgår i mit Indre!
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Når I siger: "Hor vi skal forfølge ham, Sagens Rod vil vi udfinde hos ham!"
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 så tag jer i Vare for Sværdet; thi Vrede rammer de lovløse, at I skal kende, der kommer en Dom!
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”