< Job 14 >

1 Mennesket, født af en Kvinde, hans Liv er stakket, han mættes af Uro;
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 han spirer som Blomsten og visner, flyr som Skyggen, står ikke fast.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Og på ham vil du rette dit Øje, ham vil du stævne for Retten!
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Ja, kunde der komme en ren af en uren! Nej, end ikke een!
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Når hans Dages Tal er fastsat, hans Måneder talt hos dig, og du har sat ham en uoverskridelig Grænse,
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 tag så dit Øje fra ham, lad ham i Fred, at han kan nyde sin Dag som en Daglejer!
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 Thi for et Træ er der Håb: Fældes det, skyder det atter, det fattes ej nye Skud;
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 ældes end Roden i Jorden, dør end Stubben i Mulde:
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 lugter det Vand, får det nye Skud, skyder Grene som nyplantet Træ;
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 men dør en Mand, er det ude med ham, udånder Mennesket, hvor er han da?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 Som Vand løber ud af Søen og Floden svinder og tørres,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 så lægger Manden sig, rejser sig ikke, vågner ikke, før Himlen forgår, aldrig vækkes han af sin Søvn.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Tag dog og gem mig i Dødens Rige, skjul mig, indtil din Vrede er ovre, sæt mig en Frist og kom mig i Hu! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 Om Manden dog døde for atter at leve! Da vented jeg rolig al Stridens Tid, indtil min Afløsning kom;
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 du skulde kalde - og jeg skulde svare længes imod dine Hænders Værk!
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 Derimod tæller du nu mine Skridt, du tilgiver ikke min Synd,
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 forseglet ligger min Brøde i Posen, og over min Skyld har du lukket til.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 Nej, ligesom Bjerget skrider og falder, som Klippen rokkes fra Grunden,
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 som Vandet udhuler Sten og Plaskregn bortskyller Jord, så har du udslukt Menneskets Håb.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 For evigt slår du ham ned, han går bort, skamskænder hans Ansigt og lader ham fare.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 Hans Sønner hædres, han ved det ikke, de synker i Ringhed, han mærker det ikke;
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 ikkun hans eget Kød volder Smerte, ikkun hans egen Sjæl volder Sorg.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >