< Jeremias 40 >

1 Det Ord, som kom fra HERREN til Jeremias, efter at livvagtens øverste Nebuzaradan havde løsladt ham i Rama; han lod ham hente, medens han var bundet med Lænker iblandt alle Fangerne fra Jerusalem, og Juda, der førtes til Babel.
Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
2 Livvagts øverste lod Jeremias hente og sagde til ham: "HERREN din Gud har udtalt denne Ulykke over dette Sted,
Sa’ad da shugaban matsaran ya sami Irmiya sai ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ya sa wannan masifa saboda wannan wuri.
3 og HERREN lod det ske og gjorde, hvad han havde sagt, fordi I syndede mod HERREN og ikke adlød hans, Røst; derfor timedes dette eder.
Yanzu kuma Ubangiji ya cika shi; ya yi kamar yadda ya faɗa. Dukan wannan ya faru domin kun yi zunubi ga Ubangiji ba ku kuwa yi masa biyayya ba.
4 Se, nu tager jeg i Dag Lænkerne af dine Hænder. Hvis det tykkes dig godt at drage med mig til Babel, så drag med, og jeg vil have Øje med dig; men tykkes det dig ilde, så lad være! Se, hele Landet står dig åbent; gå, hvor det tykkes dig godt og ret!"
Amma yau ina’yantar da kai daga sarƙoƙin da suke a hannuwanka. Zo mu tafi Babilon, in kana so, zan kuwa lura da kai; amma in ba ka so, kada ka zo. Ga shi, dukan ƙasar tana a gabanka; ka tafi duk inda ka so.”
5 Og da han tøvede med at vende tilbage, tilføjede han: "Så vend tilbage til Gedalja Sjafans Søn Ahikams Søn, som Babels konge har sat over Judas Land, og bosæt dig hos, ham iblandt Folket, eller gå, hvor som helst det tykkes dig ret!" Og Livvagts øverste gav ham Rejsetæring og Gave og lod ham gå.
Amma, kafin Irmiya yă juya yă tafi, Nebuzaradan ya ƙara da cewa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, wanda sarkin Babilon ya naɗa a kan garuruwan Yahuda, ka zauna da shi a cikin mutane, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga dama.” Sa’an nan shugaban ya ba shi abinci da kuma kyauta sai ya bar shi ya tafi.
6 Jeremias gik da til Gedalja, Ahikams Søn, i Mizpa og bosatte sig hos ham iblandt Folket, der var levnet i Landet.
Saboda haka Irmiya ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa ya zauna tare da shi a cikin mutanen da aka bari a ƙasar.
7 Da alle Hærførerne, som var ude i åbent Land, og deres Mænd hørte, at Babels konge havde sat Gedalja, Ahikams Søn, over Landet og over Mænd, kvinder og Børn og dem af den fattige Befolkning i Landet, som ikke var ført til Babel,
Sa’ad da dukan shugabannin hafsoshin tare da mutanen da suke a karkara suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya ɗan Ahikam gwamna a kan ƙasar ya kuma sa shi ya lura da maza, mata da’ya’yan da suke mafi talauci a ƙasar da waɗanda ba a kwashe zuwa zaman bauta a Babilon ba,
8 kom de til Gedalja i Mizpa: Jisjmael Netanjas Søn Johanan Kareas Søn. Seraja Tanhumets Søn, Netofatiten Efajs Sønner og Jezanja Maakatitens Søn, med deres Mænd.
sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan da Yonatan’ya’yan Kareya, da Serahiya ɗan Tanhumet maza,’ya’yan Efai maza, mutumin Netofa, da Yezaniya ɗan mutumin Ma’aka da mutanensu.
9 Og Gedalja, Sjafans Søn Ahikams Søn, tilsvor dem og deres Mænd således: "Frygt ikke for at stå under Kaldæerne; bosæt eder i Landet og underkast eder Babels Konge, så skal det gå eder vel.
Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, ya yi rantsuwa don yă tabbatar musu da mutanensu. Ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Babiloniyawa. Ku zauna a ƙasar ku bauta wa sarkin Babilon, zai kuma yi muku amfani.
10 Se, selv bliver jeg i Mizpa for at tage mod Kaldæerne, når de kommer til os; men I skal samle Vin, Frugt og Olie i eders Kar og bo i de Byer, I tager i Eje!"
Ni kaina zan zauna a Mizfa in zama wakilinku a gaban Babiloniyawa waɗanda za su zo wurinmu, amma ku girbe ruwan inabi,’ya’yan itatuwa na kaka, da mai, ku zuba su a tulunan ajiyarku, ku kuma zauna a garuruwan da kuka ci.”
11 Og da også alle de Judæere, der var i Moab, hos Ammoniterne, i Edom og alle de andre Lande, hørte, at Babels Konge havde levnet Juda en Rest og sat Gedalja. Sjafans Søn Ahikams Søn, over dem,
Sa’ad da dukan Yahudawan da suke a Mowab, Ammon, Edom da sauran ƙasashe suka ji cewa sarkin Babilon ya bar raguwa a Yahuda ya kuma naɗa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan gwamna a kansu,
12 vendte de alle tilbage fra alle de Steder, som de var fordrevet til, og kom til Judas Land til Gedalja i Mizpa; og de indsamlede Vin og Frugt i store Måder.
sai suka dawo ƙasar Yahuda, wurin Gedaliya a Mizfa, daga dukan ƙasashen da suke a warwatse. Suka girbe ruwan inabi a yalwace da’ya’yan itatuwan kaka.
13 Men Johanan, Kareas Søn, og alle de andre Hærførere, som havde været ude i åbent Land, kom til Gedalja i Mizpa
Yohanan ɗan Kareya da dukan manyan sojoji da suke a karkara suka zo wurin Gedaliya a Mizfa
14 og sagde: "Mon du ved, at Baalis, Ammoniternes Konge, har sendt Jisjmael, Netanjas Søn, for at myrde dig?" Men Gedalja, Ahikams Søn, troede dem ikke.
suka ce masa, “Ba ka san cewa Ba’alis sarkin Ammonawa ya aiki Ishmayel ɗan Netaniya ya ɗauke ranka ba?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam bai gaskata su ba.
15 Da sagde Johanan, Kareas Søn, i al Hemmelighed til Gedalja I Mizpa: "Lad mig gå hen og myrde Jisjmael, Netanjas Søn; ingen skal få det at vide. Hvorfor skal han myrde dig, så at hele Juda, som har samlet sig om dig, splittes, og Judas Rest går til Grunde?"
Sai Yohanan ɗan Kareya ya yi wa Gedaliya a Mizfa magana a asirce ya ce, “Bari in tafi in kashe Ishmayel ɗan Netaniya, ba kuwa wanda zai sani. Me zai sa ya ɗauke ranka ya watsar da dukan Yahudawan da suka taru kewaye da kai har waɗanda suka ragu na Yahuda su hallaka?”
16 Men Gedalja, Ahikas Søn, svarede Johanan, Kareas Søn: "Det må du ikke gøre, thi du lyver om Jisjmael!"
Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohanan ɗan Kareya, “Kada ka yi irin wannan abu! Abin da kake faɗa game da Ishmayel ba gaskiya ba ne.”

< Jeremias 40 >