< Jeremias 28 >

1 Kong Zedekias af Judas fjerde regeringsår i den femte måned sagde Profeten Hananja, Azzurs Søn, fra Gibeon til mig i HERRENs Hus i Præsternes og alt Folkets Nærværelse:
A wata na biyar na wannan shekara, shekara ta huɗu, a farkon sarautar Zedekiya sarkin Yahuda, sai annabi Hananiya ɗan Azzur, wanda ya fito daga Gibeyon, ya zo wurina a gidan Ubangiji a gaban firistoci da kuma dukan mutane,
2 "Så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Jeg har sønderbrudt Babels Konges Åg.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Zan karya karkiyar sarkin Babilon.
3 Om to År fører jeg tilbage hertil alle HERRENs Huss Kar, som Kong Nebukadnezar af Babel tog herfra og førte til Babel;
Cikin shekaru biyu zan komo da dukan kayayyakin gidan Ubangiji da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe daga wannan wuri ya kai Babilon.
4 og Jojakims Søn, Kong Jekonja af Juda, og alle de landflygtige fra Juda, som kom til Babel, fører jeg tilbage hertil, lyder det fra HERREN; thi jeg sønderbryder Babels Konges Åg."
Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da kuma dukan sauran masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suka tafi Babilon,’ in ji Ubangiji, ‘gama zan karya karkiyar sarkin Babilon.’”
5 Profeten Jeremias svarede Profeten Hananja i Nærværelse af Præsterne og alt Folket, som stod i HERRENs Hus,
Sai annabi Irmiya ya amsa wa annabi Hananiya a gaban firistoci da kuma dukan mutane waɗanda suke tsaye a gidan Ubangiji.
6 således: "Amen! Måtte HERREN gøre således og stadfæste, hvad du har profeteret, og føre HERRENs Huss Kar og alle de landflygtige fra Babel tilbage hertil!
Ya ce, “Amin! Ubangiji yă sa yă zama haka! Ubangiji yă cika maganar da ka yi annabci ta wurin komo da kayayyakin gidan Ubangiji da kuma dukan masu zaman bauta zuwa wannan wuri daga Babilon.
7 Men hør dog dette Ord, som jeg vil tale til dig og alt Folket:
Duk da haka, ka saurari abin da zan faɗa a kunnenka da kuma a kunnen duka mutane,
8 De Profeter, som levede før mig og dig fra Fortids Dage, profeterede mod mange Lande og mægtige Riger om krig, Hunger og Pest;
Daga farko fari annabawan da suka riga ka da ni sun yi annabcin yaƙi, masifa da annoba a kan ƙasashe masu yawa da kuma manyan mulkoki.
9 men når en Profet profeterer om Fred, kendes den Profet, HERREN virkelig har sendt, på at hans Ord går i Opfyldelse."
Amma annabin da ya yi annabcin salama shi za a ɗauka a matsayin wanda Ubangiji ya aika in har abin da ya furta ya zama gaskiya.”
10 Så rev Profeten Hananja Ågstængerne af Profeten Jeremiass Hals og sønderbrød dem;
Sai annabi Hananiya ya cire karkiya daga wuyar annabi Irmiya ya karya ta,
11 og Hananja sagde i alt Folkets Nærværelse: "Så siger HERREN: Således sønderbryder jeg om to År Kong Nebukadnezar af Babels Åg og tager det fra alle Folkenes Hals." Men Profeten Jeremias gik sin Vej.
ya ce a gaban dukan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘A haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar sarkin Babilon daga wuyan dukan al’ummai a cikin shekaru biyu.’” Da wannan, annabi Irmiya ya yi tafiyarsa.
12 Men efter at Profeten Hananja havde sønderbrudt Ågstængerne og revet dem af Profeten Jeremiass Hals, kom HERRENs Ord til Jeremias således:
Ba a daɗe ba bayan annabi Hananiya ya karya karkiya daga wuyan annabi Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 "Gå hen og sig til Hananja: Så siger HERREN: Du har sønderbrudt Ågstænger af Træ, men jeg vil lave Ågstænger af Jern i Stedet.
“Je ka faɗa wa Hananiya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka karya karkiyar katako, amma a wurinsa za ka sami karkiyar ƙarfe.
14 Thi så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Et Jernåg lægger jeg på alle disse Folks Hals, at de må trælle for Kong Nebukadnezar af Babel; de skal trælle for ham, selv Markens Vildt har jeg givet ham."
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’”
15 Så sagde Profeten Jeremias til Profeten Hananja: "Hør, Hananja! HERREN har ikke sendt dig, og du har fået dette Folk til at slå Lid til Løgn.
Sa’an nan annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka saurara, Hananiya! Ubangiji bai aike ka ba, duk da haka ka lallashe wannan al’umma su dogara ga ƙarya.
16 Derfor, så siger HERREN: Se, jeg slænger dig bort fra Jordens Flade; du skal dø i År, thi du har prædiket Frafald fra HERREN."
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Ina shirin kawar da kai daga fuskar duniya. A wannan shekara za ka mutu, domin ka yi wa’azin tawaye a kan Ubangiji.’”
17 Og Profeten Hananja døde samme År i den syvende Måned.
A wata na bakwai na wannan shekara, annabi Hananiya ya mutu.

< Jeremias 28 >