< Jeremias 26 >
1 I Joasias's søns, kong Jojakim af Judas, første regeringstid kom dette ord fra HERREN:
A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
2 Så siger HERREN: Stå frem i Forgården til HERRENs Hus og tal til hele Juda, som kommer for at tilbede i HERRENs Hus, alle de Ord, jeg har pålagt dig at tale til dem; udelad ikke et Ord!
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
3 Måske hører de og omvender sig, hver fra sin onde Vej, så jeg kan angre det onde, jeg har i Sinde at gøre dem for deres onde Gerningers Skyld.
Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
4 Sig til dem: Så siger HERREN: Hvis I ikke hører mig og følger den Lov, jeg har forelagt eder,
Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
5 så I hører mine Tjenere Profeternes Ord, som jeg årle og silde sendte eder, skønt I ikke vilde høre,
in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
6 så gør jeg med dette Hus som med Silo og giver alle Jordens Folk denne By at forbande ved.
to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
7 Præsterne, Profeterne og alt Folket hørte nu Jeremias tale disse Ord i HERRENs Hus;
Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
8 og da Jeremias havde sagt alt, hvad HERREN havde pålagt ham at sige til alt Folket, greb Præsterne og Profeterne og alt Folket ham og sagde: "Du skal dø!
Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
9 Hvor tør du profetere i HERRENs Navn og sige: Det skal gå dette Hus som Silo, og denne By skal ødelægges, så ingen bor der!" Og alt Folket stimlede sammen om Jeremias i HERRENs Hus.
Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
10 Da Judas Fyrster hørte det, gik de fra Kongens Palads op til HERRENs Hus og tog Sæde ved Indgangen til HERRENs nye Port.
Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
11 Så sagde Præsterne og Profeterne til Fyrsterne og alt Folket: "Denne Mand har gjort halsløs Gerning, thi han har profeteret mod denne By, som I selv hørte."
Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
12 Men Jeremias sagde til Fyrsterne og alt Folket: "HERREN sendte mig for at profetere mod dette Hus og denne By alle de Ord, I hørte.
Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
13 Bedrer dog eders Veje og eders Gerninger og hør på HERREN eders Guds Røst, at HERREN må angre det onde, han har talet imod eder.
Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
14 Men se, jeg er i eders Hånd; gør med mig, hvad der er godt og billigt i eders Øjne!
Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
15 Dog skal I vide, at hvis I dræber mig, så bringer I uskyldigt Blod over eder og denne By og dens Indbyggere; thi sandelig sendte HERREN mig for at tale alle disse ord til eder."
Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
16 Da sagde Fyrsterne og alt Folket til Præsterne og Profeterne: "Denne Mand har ikke gjort halsløs Gerning, men talt til os i HERREN vor Guds Navn."
Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
17 Og nogle af Landets Ældste trådte frem og sagde til hele Folkets Forsamling:
Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
18 "Mika fra Moresjet profeterede på Kong Ezekias af Judas Tid og sagde til alt Judas Folk: Så siger Hærskarers HERRE: Zion skal pløjes som en Mark, Jerusalem blive til Grushobe, Tempelbjerget til Krathøj.
“Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
19 Mon Kong Ezekias af Juda og hele Juda dræbte ham? Frygtede de ikke HERREN og bad ham om Nåde, så HERREN angrede det onde, han havde truet dem med? Vi er ved at bringe stor Ulykke over vore Sjæle."
“Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
20 Der var også en anden Mand, som profeterede i HERRENs Navn, Urija, Sjemajas Søn, fra Kirjat Jearim; og han profeterede mod denne By og dette Land med de samme Ord som Jeremias.
(To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
21 Da Kong Jojakim og alle hans Krigsfolk og alle Fyrsterne hørte hans Ord, stod han ham efter Livet; og da Urija hørte det, blev han bange og flygtede og kom til Ægypten.
Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
22 Men Kong Jojakim sendte Folk til Ægypten; han sendte Elnatan, Akbors Søn, og nogle andre til Ægypten,
Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
23 og de bragte Urija hjem fra Ægypten og førte ham til Kong Jojakim, som lod ham hugge ned med Sværdet og hans Lig kaste hen, hvor Småfolk havde deres Grave.
Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
24 Men Ahikam, Sjafans Søn, holdt Hånden over Jeremias, så han ikke blev overgivet i Folkets Hånd og dræbt.
Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.