< Jeremias 20 >

1 Da præsten Pasjhur, Immers søn, der var overopsynsmand i HERRENs Hus, hørte Jeremias profetere således,
Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
2 slog han ham og lod ham lægge i Blokken i den øvre Benjaminsport i HERRENs Hus.
sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
3 Men da Pasjhur Dagen efter slap Jeremias ud af Blokken, sagde Jeremias til ham: HERREN kalder dig ikke Pasjhur, men: Trindt-om-er-Rædsel.
Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
4 Thi så siger HERREN: Se, jeg gør dig til Rædsel for dig selv og for alle dine Venner; de skal falde for deres Fjenders Sværd, og dine Øjne skal se det. Og hele Juda giver jeg i Babels Konges Hånd; han skal føre dem til Babel og hugge dem ned med Sværdet.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
5 Og jeg giver alt denne Bys Gods og al dens Velstand og alle dens koslelige Ting og alle Judas Kongers Skatte i deres fjenders Hånd; de skal rane dem og tage dem og føre dem til Babel.
Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
6 Og du Pasjhur og alle, der bor i dit Hus, skal gå i Fangenskab. Du skal komme til Babel; der skal du dø, og der skal du jordes sammen med alle dine Venner, for hvem du har profeteret Løgn.
Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
7 Du overtalte mig, HERRE, og jeg lod mig overtale, du tvang mig med Magt. Dagen lang er jeg til Latter, mig håner enhver.
Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
8 Thi så tit jeg faler, må jeg skrige, råbe: "Vold og Overfald!" Thi HERRENs Ord er mig Dagen lang til Skændsel og Spot.
Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
9 Men tænkte jeg: "Ej vil jeg mindes ham, ej tale mer i hans Navn," da blev det som brændende Ild i mit indre, som brand i mine Ben; jeg er træt, jeg kan ikke mere, jeg evner det ej;
Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
10 thi jeg hører mange hviske, trindt om er Rædsel: "Angiv ham!" og: "Vi vil angive ham!" Alle mine Venner lurer på et Fejltrin af mig: "Måske går han i Fælden, så vi får ham i vor Magt, og da kan vi hævne os på ham!"
Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
11 Men HERREN er med mig som en vældig Helt; derfor skal de, som forfølger mig, snuble i Afmagt, højlig beskæmmes, thi Heldet svigter dem, få Skændsel, der aldrig glemmes.
Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
12 Du Hærskarers HERRE, som prøver den retfærdige, gennemskuer Nyrer og Hjerte, lad mig skue din Hævn på dem, thi på dig har jeg væltet min Sag.
Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
13 Syng for HERREN, lovpris HERREN! Thi han redder den fattiges Sjæl af de ondes Hånd.
Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
14 Forbandet være den Dag, på hvilken jeg fødtes; den Dag, min Moder fødte mig, skal ikke velsignes.
La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
15 Forbandet den Mand, som bragte min Fader det Bud: "Et Barn, en Dreng er født dig!" og glæded ham såre.
La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
16 Det gå den Mand som Byerne, HERREN omstyrted uden Medynk; han høre Skrig ved Gry, Kampråb ved Middagstide.
Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
17 At han ej lod mig dø i Moders Liv, så min Moder var blevet min Grav og hendes Moderliv evigt svangert!
Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
18 Hvi kom jeg af Moders Liv, når jeg kun skulde opleve Møje og Harm, mine Dage svinde i Skam!
Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?

< Jeremias 20 >