< Jeremias 13 >

1 Således saghde Herren til mig: "Gå hen og køb dig et linned bælte og bind det om din lænd, lad det ikke komme i vand!"
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 Og jeg købte bæltet efter Herrens ord og bandt det om min lænd.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 Så kom HERRENs Ord atter til mig således:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 "Tag Bæltet, du købte og har om Lænden, og gå til Frat og gem det der i eu Klipperevne!"
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 Og jeg gik hen og gemte det ved Frat, som HERREN bød.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 Men lang Tid efter sagde HERREN til mig: "Gå til Frat og hent Bæltet, jeg bød dig gemme der!"
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 Og jeg gik til Frat og gravede Bæltet op, hvor jeg havde gemt det: og se, Bæltet var ødelagt og duede ikke til noget.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 Og HERRENs Ord kom til mig således:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Så siger HERREN: Således vil jeg ødelægge Judas og Jerusalems store Herlighed.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 Dette onde Folk, som vægrer sig ved at høre mine Ord og vandrer i deres Hjertes Stivsind og holder sig til andre Guder og dyrker og tilbeder dem, skal blive som dette Bælte, der ikke duer til noget.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 Thi som Bæltet slutter sig tæt til en Mands Lænd, således har jeg sluttet hele Israels Hus og hele Judas Hus tæt til mig, lyder det fra HERREN, for at de skulde være mit Folk og blive mig til Navnkundigbed, Pris og Ære; men de hørte ikke.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Og du skal sige til dette Folk: Så siger HERREN, Israels Gud: Enhver Vindunk fyldes med Vin! Og siger de til dig: "Skulde vi ikke vide, at enhver Vindunk fyldes med Vin?"
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 så svar dem: Så siger HERREN: Se, jeg vil fylde alle dette Lands Indbyggere, Kongerne, der sidder på Davids Trone, Præsterne, Profeterne og alle Jerusalems Borgere, så de hliver drukne;
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 og jeg knuser dem mod hinanden, både Fædre og Sønner, lyder det fra HERREN; uden Skånsel, Medynk og Barmhjertighed ødelægger jeg dem.
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Hør og lyt uden Hovmod, thi HERREN taler.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Lad HERREN eders Gud få Ære, før det mørkner, før I støder eders Fødder på Skumringsbjerge, så I må bie på Lys, men han gør det til Mulm, han gør det til Mørke.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 Men dersom I ikke hører, da græder min Sjæl i Løn for Hovmodets Skyld, den fælder så bitre Tåmer; mit Øje rinder med Gråd, thi HERRENs Hjord føres bort.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 Sig til Kongen og til Herskerinden: "Tag lavere Sæde, thi af eders Hoved faldt den dejlige Krone."
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 Sydlandets Byer er lukkede, ingen lukker op, hele Juda er bortført til sidste Mand.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Løft dine Øjne og se dem komme fra Nord! Hvor er den Hjord, du fik, dine dejlige Får?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 Hvad vil du sige, når du får dem til Herrer, hvem du lærte at komme til dig som Venner? Vil ikke Veer da gribe dig som Kvinde i Barnsnød?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 Og siger du i dit Hjerte: "Hvi hændtes mig dette?" For din svare Skyld blev dit Slæb løftet op, dine Hæle skændet.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 Hvis en Neger kunde skifte sin Hud, en Panter sine Striber, så kunde og I gøre godt, I Mestre i ondt!
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 Jeg spreder dem som Strå, der flyver for Ørkenens Vind:
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 det er din Lod, din tilmålte Del fra mig, så lyder det fra HERREN, fordi du lod mig gå ad Glemme og stoled på Løgn.
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 Ja, dit Slæb slår jeg over dit Ansigt, din Skam skal ses,
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 dit Ægteskabsbrud og din Vrinsken, din skamløse Utugt; på Højene og ude på Marken så jeg dine væmmelige Guder. Ve dig, Jerusalem, du bliver ej ren hvor længe endnu?
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”

< Jeremias 13 >