< Hoseas 7 >

1 Afsløret er Efraims Brøde, Samarias ondskab, thi Svig er, hvad de har for, og Tyve gør Indbrud, Ransmænd røver på Gaden.
a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
2 De tænker ej på, at jeg husker al deres Ondskab. Nu står deres Gerninger om dem, de er for mit Åsyn.
amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
3 Med ondt i Sinde glæder de Kongen, under sleske Lader Fyrster.
“Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
4 Horkarle er de alle. De ligner en gloende Ovn, som en Bager standser med at ilde, fra Æltning til Dejgen er syret.
Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
5 De gør på Kongens Dag Fyrsterne syge af Rus. Spottere giver han Hånden,
A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
6 thi lumskelig nærmed de sig. Hjertet er som en Ovn; deres Vrede sover om Natten, men brænder i Lue ved Gry.
Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
7 Som Ovnen gløder de alle, deres Herskere æder de op; alle deres Konger falder, ej en af dem påkalder mig.
Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
8 Efraim er iblandt Folkene, aflægs er han; Efraim er som en Kage, der ikke er vendt.
“Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
9 Fremmede tæred hans Kraft, han mærker det ej; hans Hår er også grånet, han mærker det ej.
Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
10 Mod Israel vidner dets Hovmod; de vendte ej om til HERREN deres Gud og søgte ham ikke trods alt.
Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
11 Efraim er som en Due, tankeløs, dum; de kalder Ægypten til Hjælp og vandrer til Assur.
“Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
12 Men medens de vandrer, kaster jeg Nettet over dem, bringer dem ned som Himlens Fugle og revser dem for deres Ondskab.
Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
13 Ve dem, fordi de veg fra mig, Død over dem for deres Frafald! Og jeg skulde genløse dem, endskønt de lyver imod mig!
Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
14 De råber ej til mig af Hjertet, når de jamrer på Lejet, sårer sig for Korn og Most og er genstridige mod mig.
Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
15 Jeg gav deres Arme Styrke, men ondt har de for imod mig.
Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
16 De vender sig, dog ej opad, de er som en slappet Bue. Deres Fyrster skal falde for Sværd ved deres Tunges Frækhed. Det spottes de for i Ægypten.
Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.

< Hoseas 7 >